Ilimi
Mutane fiye da dubu 200 muka ba taimakon Lauya – Barista Aliyu

An bayyana bukatar sake nazarin tsarin shari’ar kasan nan muddun ana bukatar rage cinkoson da ake da shi a gidajen gyaran hali da ke fadin kasan nan
Gwamnan Jihar Plateau Caleb Muftwang ya bayyana haka lokacin da kungiyar bada tallafin aikin lauya ta kasa ta ziyarce shi a gidan gwamnati
Ita dai wannan kungiyar da ke bada agajin aikin lauya ga marasa karfj da ake tuhuma da aikata wani laifi ta zamo gatan marasa gata a kasan nan.
Don tabbatar da wannan kirarin da ake yiwa kungiyar, ta ziyarci dukkanin gidajen gyaran hali da ke kasan nan domin tabbatar da ta tallafawa wadanda ke tsare ba su da karfin daukar lauyan da zai Kare su.
Gwamnan jihar Plateau ya fadawa masu ziyarar cewa, saboda rashin adalci da daidaito ya sa ake samun aikata laifuka, don haka yace akwai bukatar yiwa tsarin shari’ar kasan nan gyaran fuska don maganin wannan matsala.
Gwamnan Wanda ya bayyana takaicin sa ganin yadda ake samun cinkoso a gidajen gyaran Hali da ke kasan Nan, yace ana shirin samarda Karin gidan gyaran Hali a Jos ta Gabas.
Tunda farko shugaban masu ziyarar kuma shugaban kungiyar Barista Aliyu Abubakar yace kungiyar su ta nada agajin lauya ga mutane fiye da dubu 200 daga shekara ta 2021 zuwa bara 2023, don yayi Kiran samun goyon baya ga kungiyar domin su ci gaba da aikin su.
Yace manufar kungiyar su, ita ce su samarda wata kasa da za a ce an Sami daidaita tsakanin dukkanin ‘yan kasa
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
