Labarai
Mutane 10 Sun Mutu A Hadarin Jiragen Soji A Malaysia
Mutane goma ne suka mutu a lokacin da wasu jirage masu saukar ungulu na sojojin Malaysia biyu suka yi karo da juna, yayin wani atisaye da suke yi a yau Talata.
Babban ami’in gudanarwa na hukumar kwana-kwana da aikin ceto ta kasar, Suhaimy Mohamad Suhail ne ya tabbatar da faruwar lamarin.
Firaministan kasar Anwar Ibhrahim ya mika sakon ta’aziyarsa ga iyalan wadanda suka rasu a hadarin da ya bayyana a matsayin mai tada hankali, inda ya ce za a gudanar da bincike don gano musabbabin faruwarsa.
Ba kasafai aka cika samun aukuwar hadarin jiagen sama masu saukar ungulu a kasasshen da ke shiyyar Kudu maso Gabashin nahiyar Asiya ba, amma a watan da ya gabata, wani jirgin sama mai saukar ungulu na jami’an da ke tsaron gabar ruwan Malaysiyan yayi hadari a mashigar Malacca, duk da dai ba a samu asarar rai ba.
Haka nan a shekarar 2016, akwai mataimakin ministan kasar da ya rasu a wani hadarin jirgin sama mai saukar ungulu a jihar Sarawak da ke kasar.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
