Connect with us

Labarai

Mun Ƙarfafa Tsaron Makarantu da Kadarorin Gwamnati a Jihar Jigawa- NSCDC

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Kasa (NSCDC) ta yi bitar ayyukanta na shekarar 2025 a Jihar Jigawa, inda ta bayyana manyan nasarori da ta samu a fannin tsaro da kare muhimman kayayyakin gwamnati.

Kwamandan NSCDC na Jihar Jigawa, Muhammad Kabir Ingawa ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Dutse yayin da yake bitar ayyukan hukumar na shekarar 2025.

Dangane da gurfanar da masu laifi, Ingawa ya ce hukumar ta yi nasarar gurfanar masu laifuka 125 a gaban kotu.

A cewarsa, shari’o’in sun haɗa da laifukan lalata dukiyar jama’a, laifukan damfara ta yanar gizo, yin sojan gona da sauran laifukan da suka shafi tsaro.

Shugaban NSCDC ya ce an kama waɗanda ake zargi da lalata kayan wutar lantarki da cibiyoyin ruwa, inda darajar kayayyakin da aka lalata ta haura naira miliyan 11.

A ƙarƙashin shirin School Safe Initiative, ya ce NSCDC ta samar da tsaro ga makarantu a faɗin jihar, tare da horar da jami’an da aka tura wannan shiri domin ƙara tabbatar da tsaro a makarantu a shekarar da ake bita.

Kwamandan NSCDC ya gode wa Gwamnatin Jihar Jigawa bisa bayar da motocin aiki guda uku, tare da sauran tallafin da aka samu daga masu ruwa da tsaki a faɗin jihar.

Muhammad Ingawa ya ce ya kara da cewa an kafa cibiyar sa ido ta zamani wacce a halin ake gwajin ayyukanta.

Ya ce cibiyar za ta tattara bayanan dukkan makarantu da ke ƙarƙashin shirin, tare da tabbatar da sa ido na awanni 24 domin ingantaccen tsaro da kulawa da ayyukan makarantu.

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara