Labarai
Mun Ƙarfafa Tsaron Makarantu da Kadarorin Gwamnati a Jihar Jigawa- NSCDC
Daga Usman Muhammad Zaria
Hukumar Tsaron Farin Kaya ta Kasa (NSCDC) ta yi bitar ayyukanta na shekarar 2025 a Jihar Jigawa, inda ta bayyana manyan nasarori da ta samu a fannin tsaro da kare muhimman kayayyakin gwamnati.
Kwamandan NSCDC na Jihar Jigawa, Muhammad Kabir Ingawa ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Dutse yayin da yake bitar ayyukan hukumar na shekarar 2025.
Dangane da gurfanar da masu laifi, Ingawa ya ce hukumar ta yi nasarar gurfanar masu laifuka 125 a gaban kotu.
A cewarsa, shari’o’in sun haɗa da laifukan lalata dukiyar jama’a, laifukan damfara ta yanar gizo, yin sojan gona da sauran laifukan da suka shafi tsaro.
Shugaban NSCDC ya ce an kama waɗanda ake zargi da lalata kayan wutar lantarki da cibiyoyin ruwa, inda darajar kayayyakin da aka lalata ta haura naira miliyan 11.
A ƙarƙashin shirin School Safe Initiative, ya ce NSCDC ta samar da tsaro ga makarantu a faɗin jihar, tare da horar da jami’an da aka tura wannan shiri domin ƙara tabbatar da tsaro a makarantu a shekarar da ake bita.
Kwamandan NSCDC ya gode wa Gwamnatin Jihar Jigawa bisa bayar da motocin aiki guda uku, tare da sauran tallafin da aka samu daga masu ruwa da tsaki a faɗin jihar.
Muhammad Ingawa ya ce ya kara da cewa an kafa cibiyar sa ido ta zamani wacce a halin ake gwajin ayyukanta.
Ya ce cibiyar za ta tattara bayanan dukkan makarantu da ke ƙarƙashin shirin, tare da tabbatar da sa ido na awanni 24 domin ingantaccen tsaro da kulawa da ayyukan makarantu.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
