Connect with us

Labarai

Matashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba

Published

on

Wani matashi mai digirin na 2 a fannin Ilimin (Theology) kuma wanda ya kammala karatun Physics, mai suna Hilekann Eric, na yawo a titunan garin Jalingo, babban birnin Jihar Taraba, yana sayar da ruwan leda domin neman abin dogaro.

Ana ganin Eric yana ɗauke da kwandon ruwan leda a kansa yana kira ga masu wucewa a kan titi yana cewa, “Pure water! Ice cold! Uku na naira 100!” yayin da rana ke tsananin duka a kansa.

Lamarin ya sha bamban da irin nasarorin ilimi da ya samu a baya.

An gano Eric ne a yankin Roadblock lokacin da wakilinmu ke tattaunawa da jama’a kan aikin sake gina Gadar Namnai da Gwamnatin Tarayya ke yi.

Eric, wanda ya fito daga al’ummar Chanchanji a ƙaramar hukumar Takum ta Jihar Taraba, ya bayyana takaicinsa kan halin da yake ciki.

“Ina da digirin digirgir biyu, amma ga ni a kan titi ina sayar da ruwan leda saboda babu aikin yi. Ina ta aiki tukuru, amma duk da haka kamar ba komai na ke yi ba,” in ji shi cikin damuwa.

Ya ce rashin aikin yi na daga cikin dalilan da ke haifar da tashe-tashen hankula da aikata laifuka a wasu wurare.

“Idan gwamnati za ta duba halin da matasa ke ciki ta tallafa musu, za su iya zama mutane masu amfani ga al’umma. Akwai mutane da za su iya kafa masana’antu ɗaya ko biyu a wannan yanki domin a ɗauki matasa aiki,” in ji Eric.

Ya ƙara da cewa shi ba shi kaɗai ba ne cikin irin wannan hali, domin akwai ɗimbin matasa masu digiri da ba su da aikin yi.

“Wannan ruwan da kuke gani ina sayarwa shi ne abin da nake rayuwa da shi. Ina gode wa Allah da haka, domin ya fi na shiga sata ko wani abu na haram,” in ji shi.

Eric ya kuma bayyana cewa wasu ’yan siyasa na amfani da matasa wajen yaƙin neman zaɓe, amma bayan sun samu mulki ba su samar musu da aikin yi ba.

A cewarsa, duk da cewa gwamnati ba za ta iya ɗaukar dukkan marasa aikin yi aiki ba, kafa masana’antu kaɗan zai taimaka wajen rage matsalar.

Sai dai ya yaba wa Gwamnatin Tarayya kan bayar da kwangilar sake gina Gadar Namnai da ta rushe, yana mai cewa wannan wani muhimmin mataki ne.

Sai dai ya nuna damuwa kan hanyar zuwa ƙaramar hukumar Kurmi a jihar Taraba, wadda ya ce ta daɗe tana cikin mummunan hali amma har yanzu ba a gyara ta ba.

“Ba wai babu manyan mutane a yankin ba, akwai su. Amma har yanzu ba su gyara hanyar ba, sai dai su riƙa amfani da ita wajen yaudarar jama’a a lokacin yaƙin neman zaɓe,” in ji shi.

A halin yanzu, Hilekann Eric na ci gaba da sayar da ruwan leda tare da fatan wata rana al’amuransa za su canza.

Ya kuma bar lambar wayarsa ga duk wanda zai iya taimaka masa: 08120231338

Sani Sulaiman

Labarai

Labarai1 hour ago

An Yi Wa Jami’an FRSC A Jos Gwajin Idanu Kyauta Domin Ranar Glaucoma Ta Duniya

Jami’an kula da hanya na Hukumar Kiayyae hadura ta kasa a Jos sun samu damar yin gwajin idanu da kuma...

Labarai1 hour ago

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Fasa Kwauri Na Naira Miliyan 478 A Kwara

Hukumar Kwastam ta Najeriya, reshen Jihar Kwara, ta ce ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta da kuma...

Labarai1 hour ago

Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Yi Rijista a Jam’iyyar APC

Mataimakin Gwamnan Jihar Zamfara, Malam Mani Malam Mummuni, ya yi rijista a hukumance a matsayin cikakken ɗan jam’iyyar APC. An...

Labarai1 hour ago

Jami’ar Bayero Kano Ta Yi Martani Kan Zargin Damfarar Dalibi

Jami’ar Bayero Kano (BUK) ta yi martani kan zarge-zargen da ke yawo cewa wani mutum da ake zargin yana ikirarin...

Labarai2 hours ago

Matashi Mai Digiri Na Farko Na Sayar Da Ruwan Leda A Taraba

Wani matashi mai digirin na 2 a fannin Ilimin (Theology) kuma wanda ya kammala karatun Physics, mai suna Hilekann Eric,...

Labarai2 days ago

Tinubu Ya Nada Lamido Yuguda Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa

Daga Bello Wakili Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya nada Lamido Abubakar Yuguda a matsayin Mataimakin Gwamnan Babban Bankin Kasa CBN,...

Labarai2 days ago

An Nada Kabir Yahaya Darakta Janar na Farko na Filin Jirgin Sama da ke Gusau

Daga Aminu Dalhatu Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗin Kabir Yahaya Gusau a matsayin Darakta Janar na...

Labarai2 days ago

Kwastam ta Kama Kayayyaki na Sama da Naira Miliyan 478 a Jihar Kwara

Daga Ali Muhammad Rabi’u  Hukumar Kwastam ta Kasa reshen Jihar Kwara ta kama tare da kwace kayayyakin da aka haramta...

Labarai3 days ago

NEMA Da Masu Ruwa Da Tsaki Sun Kara Haɗa Gwiwa Don Hana Aukuwar Ambaliya Da Hadarin Tankar Mai

  By Adamu Yusuf   Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), tare da haɗin gwiwar masu ruwa da...

Labarai4 days ago

Kaduna Ta Kaddamarda Shirin Rabon Maganin Kariya Daga Cutar Dundumi

  Daga Khadija Kubau   Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kaduna tareda haɗin gwiwar kungiyar Sightsavers sun kaddamar da shirin raba...

Mafi Shahara