Labarai
Matasan Kauru Sun Yi Allah-wadai da Mulkin Ƙarfi, Sun Buƙaci Adalci da Haɗin Kai
Daga Yusuf Zubairu
Wata ƙungiyar matasa a Ƙaramar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna ta bayyana cewa shugabanci na bai-ɗaya ba tare da nuna rinjaye a bangare daya ba, shi ne ginshikin dorewar dimokuraɗiyya da haɗin kan al’umma a yankin.
Ƙungiyar, wato Kauru Youth Ambassadors (KYA) ta yi wannan kira ne yayin mayar da martani ga kalaman wani mai suna Musa Waziri ne a wani bidiyo da ya karade kafafen yanar gizo, inda ta jaddada cewa Kauru ta ƙunshi sassa uku ne da suka hada da Masarautar Kauru, Sarautar Kumana da Sarautar Chawai.
A cewar ƙungiyar, kowanne daga cikin waɗannan sassa uku na da masu ilimi, ƙwarewa da kishin ƙasa, waɗanda suka cancanci rike muƙamai a kowane fanni.
Da yake magana a madadin KYA, Kwamared Junaidu Ishaq Maisalati ya ce ƙungiyar ta soki ikirarin Waziri na cewa “ana ƙwace iko ne, ba a bayar da shi ba,” inda ya bayyana cewa mafi akasari siyasa na karkata ne ga waɗanda ke da rinjayen yawan jama’a, da albarkatun kasa da damar shiga tsarin jam’iyya.
Ya bayyana cewa tsarin raba mulki (zoning) ba wajibi ba ne a harkar siyasa, illa hanya ce ta kaucewa watsi da wani yanki, tare da tabbatar da wakilci na adalci a al’umma mai bambance-bambance kamar Kauru.
Ƙungiyar ta kuma bayyana cewa ba daidai ba ne a ce tsarin karba-karba wato zoning na haifar da shugabanni marasa ƙwarewa, alhali kuma ana da tabbacin cewa akwai ƙwararru a dukkan sassan Kauru.
Ta jaddada cewa tsarin na karba-karba ba ya rage ƙa’idar shugabanci, sai dai yana ƙarfafa kowanne yanki ne ya gabatar da mafi cancantar ’ya’yansa idan aka ba shi dama.
A cewar ƙungiyar, mulki na karba karba yana ƙarfafa tarbiyyar shugabanci, gina ƙwarewa da kuma ƙarfafa cibiyoyin siyasa.
Saboda haka, ta yi gargaɗi cewa ci gaba da keɓance wasu sassa na iya haifar da rashin yarda, sakaci da ɓacin rai, wanda hakan ke tauye ci gaba da haɗin kan al’umma.
Ƙungiyar Kauru Youth Ambassadors (KYA) ta nanata cewa ya zama wajibi a tabbatar da adalci domin samun haɗin kai, zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa a Kauru.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
