Connect with us

Labarai

Matasan Kauru Sun Yi Allah-wadai da Mulkin Ƙarfi, Sun Buƙaci Adalci da Haɗin Kai

Published

on

 

Daga Yusuf Zubairu

Wata ƙungiyar matasa a Ƙaramar Hukumar Kauru ta Jihar Kaduna ta bayyana cewa shugabanci na bai-ɗaya ba tare da nuna rinjaye a bangare daya ba, shi ne ginshikin dorewar dimokuraɗiyya da haɗin kan al’umma a yankin.

Ƙungiyar, wato Kauru Youth Ambassadors (KYA) ta yi wannan kira ne yayin mayar da martani ga kalaman wani mai suna Musa Waziri ne a wani bidiyo da ya karade kafafen yanar gizo, inda ta jaddada cewa Kauru ta ƙunshi sassa uku ne da suka hada da  Masarautar Kauru, Sarautar Kumana da Sarautar Chawai.

A cewar ƙungiyar, kowanne daga cikin waɗannan sassa uku na da masu ilimi, ƙwarewa da kishin ƙasa, waɗanda suka cancanci rike muƙamai a kowane fanni.

Da yake magana a madadin KYA, Kwamared Junaidu Ishaq Maisalati ya ce ƙungiyar ta soki ikirarin Waziri na cewa “ana ƙwace iko ne, ba a bayar da shi ba,” inda ya bayyana cewa mafi akasari  siyasa na karkata ne ga waɗanda ke da rinjayen yawan jama’a, da albarkatun kasa da damar shiga tsarin jam’iyya.

Ya bayyana cewa tsarin raba mulki (zoning) ba wajibi ba ne a harkar siyasa, illa hanya ce ta kaucewa watsi da wani yanki, tare da tabbatar da wakilci na adalci a al’umma mai bambance-bambance kamar Kauru.

Ƙungiyar ta kuma bayyana cewa ba daidai ba ne a ce tsarin karba-karba wato zoning na haifar da shugabanni marasa ƙwarewa, alhali kuma ana da tabbacin cewa akwai ƙwararru a dukkan sassan Kauru.

Ta jaddada cewa tsarin na karba-karba ba ya rage ƙa’idar shugabanci, sai dai yana ƙarfafa kowanne yanki ne ya gabatar da mafi cancantar ’ya’yansa idan aka ba shi dama.

A cewar ƙungiyar, mulki na karba karba  yana ƙarfafa tarbiyyar shugabanci, gina ƙwarewa da kuma ƙarfafa cibiyoyin siyasa.

Saboda haka, ta yi gargaɗi cewa ci gaba da keɓance wasu sassa na iya haifar da rashin yarda, sakaci da ɓacin rai, wanda hakan ke tauye ci gaba da haɗin kan al’umma.

Ƙungiyar Kauru Youth Ambassadors (KYA) ta nanata cewa ya zama wajibi a tabbatar da adalci domin samun haɗin kai, zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa a Kauru.

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara