Labarai
Mataimakin Shugaban Tanzaniya Na Barazanar Yin Murabus Saboda Matsalar Karancin Ruwa
Mataimakin shugaban ƙasar Tanzaniya, Phillip Mpango ya yi barazanar sauka daga muƙaminsa saboda matsalar ƙarancin ruwan sha da aka daɗe ana fama da ita a lardin Mwanga da ke arewacin ƙasar.
Mista Mpango ya zargi ƴan kwangilar da ke kula da muhimmin aikin samar da ruwan sha a yankin na ɗaukan lokaci kafin kammala shi.
Shirin na sama da dala dubu 100 an soma shi ne kusan shekara 20 da ta gabata, a cewar Mista Mpango.
“Idan har aikin nan ba zai samar da ruwa ba ga mutanen yankin nan da watan Yuni, zan sauka.” Inji Mista Mpango.
“Ba zan sake zuwa nan na faɗa wa jama’a su ƙara hakuri ba, ruwa shi ne rayuwa,” ya ce.
A cewar jami’an gwamnati da suka yi wa Mista Mpango rakiya zuwa Mwanga a ranar Alhamis, an yi kashi 90 cikin 100 na aikin samar da ruwan.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
