Connect with us

Kasuwanci

Mata Da Matasa Dari Hudu Suka Amfana Da Tallafi A Gandun Albasa Kano

Published

on

An bukaci masu hannu da shuni da ‘yan kasuwa da ma daidaikun jama’a su rika tallafawa mata da matasa da dukkanin abin da Allah ya hore mu domin ganin sun iya dogara da kansu.

Kogunan Kasar Hausa Alhaji Aliyu Da’u Abubakar ne yayi wannan kiran a wajen bada tallafi ga mata da matasa fiye da dari hudu da Kungiyar Matasan Abban Gandun Albasa Kano ta shirya a Kano.

Kogunan Kasar Hausa ya bayyana cewa irin wannan tallafi zai taimaka matukar gaske wajen karfafa mata da matasa su tsaye da kafafun su.

Yayi bayanin cewa babu shakka wadannan matasan zasu dogara da kansu kana da daukar dawainiyar iyalansu da wannan tallafi.

Taron da aka gudanar a asabar ta karshen mako ya shedi yadda mata da matasa suka sami tallafi kudi daga Naira dubu goma zuwa ashirin dai dai da yadda Allah ya tsaga da rabon mutum.

Wannan tallafin da aka ba masu kananan sana’o’i zai taimaka matukar gaske a cewa Uban Taron kuma Kogunan Kasar Hausa Alhaji Aliyu Da’u Abubakar lokacin da yake magana da Radiyo Nijeriya Kaduna.

Daga cikin wadanda suka amfani da wannan tallafin wacce tayi magana a madadin dukkanin wadanda suka amfana Zainab Adamu tayi godiya ga Kungiyar Matasan Matasan Abban Gandun Albashi da wannan jinkai da ya musu.
Cov/Zainab Adamu

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara