Labarai
Manoman Shinkafa Za Su Amfana Da Shiri Na Musamman Da Gwamnatin Jigawa Ta Bullo Da Shi
Gwamnatin Jihar Jigawa ta bukaci manoman shinkafa da su hanzarta gyaran gonakinsu domin samun damar shiga shirin noman shinkafa da Gwamna Umar Namadi ya bullo da shi domin samar da abinci da kuma bunkasa tattalin arzikin jihar.
Mai bai wa Gwamna shawara kan shirin Noma Dan Riba, Alhaji Muhammad Idris Danzomo ya bada wannan shawara a zantawarsa da manema labarai a Dutse.
Ya ce bukatar ta zama wajibi domin bai wa manoman damar amfana da tsare tsaren gwamnati na bunkasa noman shinkafa da samar da ayyukan yi ga al’umma.
Alhaji Muhammad Idris Danzomo ya kuma shawarci manoman na shinkafa da su tabbatar sun tona rijiya a gonakinsu.
A cewar sa, za a tura malaman gona zuwa lungu da sako domin zakulo manoman shinkafar da suka shirya domin cin gajiyar sharin.
Bunkasa aikin gona dai na daya daga cikin kudirori 12 na Gwamna Umar Namadi na bunkasa tattalin arzikin al’umma da na gwamnati.
Usman Mohammed Zarian
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
