Connect with us

Kasuwanci

Majalisar Kano Ta Karyata Binciken Shugabar ALGON

Published

on

Majalisar dokokin jihar Kano ta karyata rahotannin da ke cewa ta kaddamar da bincike kan Hajiya Sa’adatu Yusha’u, shugabar karamar hukumar Tudun Wada kuma shugabar kungiyar ALGON a jihar.

 

A cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun babban sakataren yada labarai na kakakin majalisar, Kamaludeen Sani Shawai, majalisar ta bayyana ikirarin da aka yi a matsayin “marasa tushe, yaudara, kuma gaba daya karya.”

 

Majalisar ta fayyace cewa Shugaban Masu Rinjaye, Alhaji Lawan Hussaini Dala bai bayar da wata tattaunawa ba ko kuma ya yi magana a bainar jama’a dangane da fara wani bincike a kan Shugaban ALGON.

 

“Hon. Dala, kamar kowane zababben mamba, kundin tsarin mulki ya ba shi ikon karbar koke daga mazabu. Karbar koke ba ya nufin amincewa da abin da ke cikinta ko kuma wani mataki na doka,” in ji sanarwar.

 

Majalisar ta kuma yi gargadin cewa rahotannin da ake ta yadawa, musamman ma daga majiyoyin da ba na hukuma ba, suna nuna bata-gari ne na tsarin dokoki, kuma da alama wani shiri ne na lalata mutuncin Shugaban masu rinjaye.

 

Da take jaddada kudurinta na bin ka’ida, majalisar ta tunatar da jama’a cewa babu wani bincike da zai iya ci gaba ba tare da bin ka’idojin da aka kafa ba, ciki har da yin adalci ga duk bangarorin da abin ya shafa.

 

Ya yi Allah wadai da yada zarge-zarge marasa tushe ba tare da wata shaida ko tabbaci daga wata majiya ta Majalisar ba.

 

Sanarwar ta karkare da gargadi ga kafafen yada labarai da kuma daidaikun mutanen da ke da hannu wajen yada labaran karya:

“Muna bukatar a ba mu hakuri da kuma janye cikakken labarin da aka kirkiro a cikin kwanaki bakwai (7). Rashin bin wannan doka na iya haifar da hukuncin shari’a .”

 

Khadija Aliyu/Kano

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara