Connect with us

Labarai

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Kirikasamma

Published

on

Kwamatin kananan hukumomi na Majalisar Dokokin jihar Jigawa ya duba ayyukan raya kasa da karamar hukumar Kirikasamma ta samu nasarar gudanarwa daga watan Oktobar 2024 kawo yanzu.

Shugaban Kwamatin, Alhaji Aminu Zakari, ya kafa kananan kwamitoci guda biyu domin samun nasarar tantance ayyukan a cikin garin   Kirikasamma da kauyuka.

Karamin Kwamati na daya bisa jagorancin wakilin mazabar
Kanya Babba Alhaji Ibrahim Hashimu Kanya, ya duba aikin sanya soma da tona riniyar tuka tuka a mayanka da magudanin ruwa a garin Marma da aikin gina rumfunan kasuwa a garuruwan Tasheguwa, Marma, Dilmari da Madaci.

Alhaji Ibrahim Hashim Kanya ya bayyana wa shugaban kamsilolin karamar hukumar wanda ke yiwa tawagar rakiya, Malam Isyaku Abdullahi, muhimmancin ziyarar duba ayyukan Gwamnati dan tabbatar da inganci.

Sai Kuma karamin Kwamati na biyu bisa jagorancin wakilin mazabar Kiyawa Alhaji Yahaya Muhammad Andaza wanda ya duba aikin gyaran hanyar Gafta zuwa Baturiya akan fiye da naira milyan 4 da dubu dari 2, wadda ambaliyar ruwa ta lalata a daminar bara da kuma aikin gina rumfar kasuwa a garin Baturiya.

Tun da farko a sakatariyar karamar hukumar Kirikasamma, Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar Dokokin jihar Jigawa Kuma wakilin mazabar Gwiwa,
Alhaji Aminu Zakari ya ce ziyarar Kwamatin na daga nauyin da tsarin mulki ya dorawa bangaren majalisa wajen duba manufofi da shiryeyen Gwamnati baya da yin doka da amincewa da kasafin kudin kowacce shekara.

Alhaji Aminu Zakari ya ce Kwamatin Yana duba kundin bayanan harkokin Kudi da na sha’anin Mulki da su ka hadar da littafin shiga da fitar kudade da takardun biyan kudade na voucher da alkaluman tattara kudaden shiga da kundin tarukan kwamitocin karamar hukuma domin tabbatar da kashe kudaden Gwamnati ta hanyar da ta dace domin wanzuwar shugabanci nagari.

A cewar sa, daga yanzu Daraktan tsare-tsare ya zamo daga cikin masu rattaba hannu kan takardun kashe kudade, mataimakin shugaban karamar hukumar zai rike sashen kula da ruwa da tsafta a matsayin Kansila maras gafaka.

Yayi nuni da cewar, akwai bukatar karamar hukumar ta gina ajujuwa guda 2 na makarantun ‘ya’Yan fulani makiyaya domin shigo da su cikin tsare tsaren ci gaban al’umma.

A nasa jawabin, shugaban karamar hukumar Kirikasamma, Alhaji Muhammad Maji Wakili Marma, ya lura da gudummawar da bangaren majalisa ke bayarwa wajen gudanar da harkokin Gwamnati a matakin jiha da kananan hukumomi.

Alhaji Maji Wakili ya bada tabbacin aiki da shawarwari Kwamatin domin karfafa matarka cigaban karamar hukumar.

Sauran Yan Kwamatin sun hadar da mataimakin shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Kaugama Alhaji Sani Sale Zaburan da sakataren Kwamatin Kuma Akawun Majalisa Alhaji Yusha’u Muhammad, da oditoci biyu da mataimakan sakatare.

 

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai11 hours ago

Ana Zargin Mutum 140 Sun Bace Bayan Nutsewar Jirgin Ruwan Iran a Gaɓar Sri Lanka

Rundunar sojin ruwan Sri Lanka ta tabbatar da ceto mutum 32 bayan samun kiran gaggawa daga jirgin ruwan sojin Iran...

Ilimi11 hours ago

Gwamnatin Tarayya da ke Gusau za ta Kafa Cibiyar Nazari kan Tarihi da Al’adun Zamfara

Daga Aminu Dalhatu  Shugaban Jami’ar Tarayya da ke Gusau (FUGUS), Farfesa Tukur Adamu, ya sanar da shirin jami’ar na kafa...

Labarai11 hours ago

Jam’iyyar APC Ta Zaɓi Sabbin Shugabanni a Jihar Kano

Daga Abdullahi Jalaluddeen Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a Jihar Kano ta zaɓi sabbin shugabanni domin jagorantar harkokin jam’iyyar. Zaɓen,...

Labarai13 hours ago

Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Miliyoyin Naira Don Sayen Gidaje 96 Daga Gwamnatin Tarayya

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da kashe sama da Naira Miliyan 853 domin sayen gidaje guda...

Labarai1 day ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai2 days ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai3 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Mafi Shahara