Connect with us

Labarai

Majalisar Dattijan Na So A Bai Wa Kananan Hukumomi Yancin Kai

Published

on

Majalisar Dattijan Najeriya ta nemi Shugaba Tinubu ya shige gaba domin nema wa kananan hukumomi ‘yanci a wajen jihohi, wanda suka ce hakan zai iya magance matsalar tsaro da ake fama da ita da tururuwar da mutane ke yi zuwa birane da kuma rashin aikin yi.

Sanata Abdurrahaman Kawu Sumaila ne ya gabatar da kudurin wanda ya ce akwai bukatar a zauna da gwamnoni da masu ruwa da tsaki domin tattauna yadda za a yi kananan hukumomi su samu ‘yancinsu da suka rasa a baya.

Kawu Sumaila ya ce a wannan lokacin za a samu nasara saboda salon da majalisar ta dauka a wannan karon ya sha banban da matakan da aka rika dauka a baya.

Sanatan ya ce sun nemi shugaban kas aya shige gaba wajen tabbatar da an samu abinda ake so, ta hanyar kiran taron masu ruwa da tsaki da zai kunshi gwamnoni da ýan majalisu na tarayya da na jihohi da shugabannin al’umma da malaman addini da sauransu domin a tattauna domin samarwa kananan hukumomi matsaya guda.

Kawu Sumaila ya ce idan har aka samu nasarar daukar matakin za a samu saukin rashin tsaro da talauci da ya addabi jihohin arewacin Najeriya, ” A cikin wata uku abubuwa za su canja, idan aka ce a karamar hukuma za a yi tasarrafin miliyan 300 ko miliyan 400, bayan an biya ma’aikata duk wasu kananan ayyuka za a yi.”

Sanata Kawu ya ce ba abin birgewa ba ne ace anyi zabe amman jam’iya guda za ta lashe zaben kananan hukumomi ” kai an zabe ka, yan majalisar jihohin ka daga jam’iyu daban-daban, amman ranar zaben kananan hukumomi jam’iya guda za ta lashe, kai kasan ba gaskiya ake yi ba”.

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara