Connect with us

Labarai

Ma’aikatar Lafiya Ta Fara Daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa a Jigawa

Published

on

Usman Muhammad Zaria 

Ma’aikatar Lafiya ta kasa karkashin shirin kula da lafiya na SWAP ta fara aikin daukar Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa wato (National Health Fellows) a Jihar Jigawa.

Da yake jawabi jim kaɗan bayan kammala aikin, Mataimakin Darakta kuma Mai Taimaka wa Darakta-Janar na Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Kasa, Dakta Jibrin Muhammad Bashar, ya bayyana cewa aikin daukar ma’aikatan wani shiri ne na Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya karkashin jagorancin Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate.

Dakta Bashar, wanda kuma shi ne Babban Mai Kula da aikin daukar ma’aikatan a Jihar Jigawa, ya bayyana cewa shirin na da nufin zaben Jami’an Kula da Lafiya na Ƙasa da za su rika sa ido kan aiwatar da Asusun Kula da Lafiya na Asali (Basic Health Care Provision Fund) a cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko a fadin jihar.

A cewarsa, wadannan ma’aikata za su kasance jakadu na Asusun Kula da Lafiya na Gwamnatin Tarayya, wanda Hukumar Kula da Kiwon Lafiya ta Matakin Farko ta Kasa (National Primary Health Care Development Agency) ke kula da shi.

Ya kara da cewa an kirkiri asusun ne domin tallafa wa rukunin al’umma masu rauni, ciki har da mata, yara da tsofaffi, ta hanyar samar da muhimman ayyukan kiwon lafiya da kuma tallafin kudi.

Ya bayyana cewa za a zabi mutum ashirin da bakwai, inda kowane daya zai wakilci daya daga cikin kananan hukumomi ashirin da bakwai na Jihar Jigawa.

Dakta Bashar ya nuna gamsuwa da yadda aka gudanar da aikin daukar ma’aikatan, inda ya yaba wa kwamitin daukar ma’aikata na jihar da kwamitin  bisa kwarewa, gaskiya da kuma rashin nuna bangaranci yayin aikin.

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara