Labarai
Ma’aikatan Ceto Na Cigaba Da Neman Jirgin Shugaban Kasar Iran Da Ya Bace
Da yammacin yau lahadi ne tarin ma’aikatan ceto suka bazama wajen aiki gano jirgi mai saukar ungulu dauke da shugaba Ebrahim Raïsi na Iran, wanda wani “hatsari” ya rutsa da shi, kamar yadda jami’ai da kafafen yada labaran kasar suka sanar.
An kaddamar da bincike don gano jirgin mai saukar ungulu amma ya yi wuya saboda “yanayi mara kyau”, ciki har da hazo, in ji ministan cikin gida Ahmed Vahidi a gidan talabijin na kasar.
Jirgin na shugaba Raïsi na daya daga cikin ayarin jirage masu saukar ungulu uku dauke da tawagar shugaban kasar.
“Zai iya ɗaukar lokaci kafin a isa yankin da wannan jirgi ya fadi ,” in ji ministan cikin gida Ahmed Vahidi, kodayake wannan wurin zai kasance a cikin dajin Dizmar, kusa da garin Varzaghan.
Ebrahim Raïssi ya ziyarci lardin gabashin Azarbaijan a yau lahadi, inda ya kaddamar da wata madatsar ruwa tare da shugaban kasar Azarbaijan Ilham Aliev a kan iyakar kasashen biyu.
Raïssi, mai shekaru 63 , ya kasance shugaban Jamhuriyar Iran tun watan Yunin 2021.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
