Connect with us

Labarai

Libya Ta Tasa Keyar Baƙin Haure Yan Kasar Sudan 700 Zuwa Kasarsu

Published

on

Gwamnatin Libya ta tasa keya daruruwan baƙin haure ‘yan ƙasar Sudan 700 zuwa ƙasarsu da yaƙi ya ɗaiɗaita, A cewar mahukuntan, waɗannan mutanen sun yi hijira zuwa Libya ne domin gujewa yaƙi da talauci, inda suke neman hanyar tsallakawa zuwa Turai.

A cewar huƙumar kula da baƙin haure, an kori mutane 700 daga Libya da aka kama a tsakiya da kudu maso gabashin ƙasar, inda aka tura su zuwa Sudan a ranar Juma’ar da ta gabata ta ƙasa.

Bayanin ya nuna cewa wasu daga cikin waɗanda aka korar na ɗauke da cututtuka masu yaɗuwa kamar su hepatitis da cuta mai karya garkuwar jiki, wasu kuma an tura su ne saboda laifuffuka ko kuma dalilan tsaro.

Korar ta zo ne a lokacin da mahuƙuntan ke ci gaba da yaƙi da safarar mutane a gabashin Libya, wanda ke ƙarƙashin ikon kwamandan sojoji Khalifa Hiftar.

A makon da ya gabata, masu tsaron gaɓar teku a gabashin Libya sun kame wani jirgin ruwa da ke ɗauke da baƙin haure 80 da ke neman zuwa ƙasashen ƙetare, a gabashin birnin Tobruk.

Yaƙin da hukumomin ke yi sun haɗa da kai hare-hare kan wuraren da ake safarar mutane a gabashi da kudancin Libya. A farkon wannan watan, an ƙwato baƙin haure ‘yan Sudan 104, ciki har da mata da yara, da aka tsare a gidan da ake tara mutane da ake fataucin su a birnin Ajdabiya, mai nisan kilomita 800 daga babban birnin Tripoli, a cewar ƴan sa kai na yankin.

Libya ta zama hanyar wucewa ga mutanen da ke guje wa yaƙi da talauci a yankunan gabas ta tsakiya da Afirka, inda suke neman rayuwa mai kyau a Turai.

Masu safarar mutane sun ci gajiyar rashin kwanciyar hankali a Libya tsawon shekaru goma, inda suke shigar da baƙin haure ta iyakokin ƙasar da suka haɗa da ƙasashen Chadi da Nijar da Sudan da Masar da Aljeriya da kuma Tunisiya.

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara