Labarai
Libya Ta Tasa Keyar Baƙin Haure Yan Kasar Sudan 700 Zuwa Kasarsu
Gwamnatin Libya ta tasa keya daruruwan baƙin haure ‘yan ƙasar Sudan 700 zuwa ƙasarsu da yaƙi ya ɗaiɗaita, A cewar mahukuntan, waɗannan mutanen sun yi hijira zuwa Libya ne domin gujewa yaƙi da talauci, inda suke neman hanyar tsallakawa zuwa Turai.
A cewar huƙumar kula da baƙin haure, an kori mutane 700 daga Libya da aka kama a tsakiya da kudu maso gabashin ƙasar, inda aka tura su zuwa Sudan a ranar Juma’ar da ta gabata ta ƙasa.
Bayanin ya nuna cewa wasu daga cikin waɗanda aka korar na ɗauke da cututtuka masu yaɗuwa kamar su hepatitis da cuta mai karya garkuwar jiki, wasu kuma an tura su ne saboda laifuffuka ko kuma dalilan tsaro.
Korar ta zo ne a lokacin da mahuƙuntan ke ci gaba da yaƙi da safarar mutane a gabashin Libya, wanda ke ƙarƙashin ikon kwamandan sojoji Khalifa Hiftar.
A makon da ya gabata, masu tsaron gaɓar teku a gabashin Libya sun kame wani jirgin ruwa da ke ɗauke da baƙin haure 80 da ke neman zuwa ƙasashen ƙetare, a gabashin birnin Tobruk.
Yaƙin da hukumomin ke yi sun haɗa da kai hare-hare kan wuraren da ake safarar mutane a gabashi da kudancin Libya. A farkon wannan watan, an ƙwato baƙin haure ‘yan Sudan 104, ciki har da mata da yara, da aka tsare a gidan da ake tara mutane da ake fataucin su a birnin Ajdabiya, mai nisan kilomita 800 daga babban birnin Tripoli, a cewar ƴan sa kai na yankin.
Libya ta zama hanyar wucewa ga mutanen da ke guje wa yaƙi da talauci a yankunan gabas ta tsakiya da Afirka, inda suke neman rayuwa mai kyau a Turai.
Masu safarar mutane sun ci gajiyar rashin kwanciyar hankali a Libya tsawon shekaru goma, inda suke shigar da baƙin haure ta iyakokin ƙasar da suka haɗa da ƙasashen Chadi da Nijar da Sudan da Masar da Aljeriya da kuma Tunisiya.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
