Connect with us

Labarai

KWEPA Ta Rufe Otel Takwas A Ilori

Published

on

Hukumar Kare Muhalli ta Jihar Kwara (KWEPA) ta rufe otel guda takwas a Ilori saboda kin bin ƙa’idojin da aka kafa na gudanar da harkokin otel a jihar.

Da yake magana kan lamarin a Ilorin, babban manajan hukumar, Jide Aina, ya bayyana cewa wannan matakin ya biyo bayan sanarwa da gargaɗi da dama da aka aika musu tun da farko.

Babban Manajan wanda shugaban sashen kula da otel, Malam Aminullahi AbdulRahman ya wakilta, ya ce an ba wa waɗannan otel ɗin isasshen lokaci don gyara ayyukansu, amma suka ci gaba da yin watsi da umarnin hukumar.

Ya jaddada cewa an ɗauki wannan mataki ne bisa ga dokar muhalli ta jihar Kwara, inda ya ce ba a yi hakan da wata mummunar manufa ba, sai dai mataki ne da ya zama wajibi domin dakile karya doka da kuma kiyaye ƙa’idojin kiwon lafiya.

Jide Aina ya kuma bayyana cewa tilasta bin doka a sashen harkokin otel zai taimaka wajen kare rayuwar mazauna yankin, inganta lafiyar jama’a, da kuma samar da yanayi mai kyau ga masu saka hannun jari da masu yawon buɗe ido.

Babban manajan ya sake tabbatar da jajircewar hukumar wajen yin haɗin gwiwa da masu ruwa da tsaki a fannin harkokin otel domin inganta ci gaban ɗorewa da kuma ɗaukar alhakin kare muhalli a jihar.

Ya kuma ja hankalin sauran masu harkokin otel da su bi ƙa’idojin muhalli da na gudanarwa gaba ɗaya don kauce wa irin wannan mataki.

 

Ali Muhammad Rabi’u

 

 

Labarai

Labarai14 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara