Labarai
Za Mu Yaki Ayyukan Ta’addanci A Jihar Kano – Sabon Kwamishina
Kwamishinan ‘yan sanda na Jihar Kano CP Salman Dogo Garba, ya fara sintiri a yankunan da ‘yan daba suka sake kunno kai a wasu sassan birnin Kano, tare da tabbatar wa mazauna yankunan kudurinsa na wanzar da zaman lafiya.
CP Dogo Garba ya nemi hadin kan shugabannin al’umma da jami’an ‘yan sanda na yanki (DPOs) don tsara dabarun yakar wannan barazana da kuma dawo da tsaro.

Ya jaddada cewa tsaro hakki ne ya rataya a wuyan kowa, don haka ya bukaci jama’a da su kai rahoton duk wata barazana da ka iya kunno kai ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa da su ko kuma ta lambobin gaggawa.
CP ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan abubuwan da suka faru a baya-bayan nan, kuma ana kokarin kamo masu aikata laifin da masu daukar nauyinsu.
Ya yaba da goyon bayan mazauna yankin masu son zaman lafiya, inda ya bukaci a ci gaba da ba da hadin kai.
Abdullahi Jalaluddeen
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
