Connect with us

Labarai

Kungiyar AFAN Ta Shirya Taron Bita Ga Manoman Jihar Jigawa

Published

on

Hadaddiyar kungiyar manoma ta kasa reshen Jihar Jigawa da cibiyar binciken yanayin kasa dake Kaduna sun shirya wa manoma daga wasu kananan hukumomin Jihar Jigawa taron karawa juna sani na yini biyu akan gwajin yanayin karfin kasa kafin manomi ya yi shuka a gona.

Da yake jawabi yayin bude bitar, Farfesa Uzaifatu Karfi na tsangayar aikin gona dake Jami’ar tarayya ta Dutse, ya ce yin gwajin yanayin karfin kasa kafin yin shuka zai tantance wace irin shuka ya dace a yi da za ta bada yabanya mai kyau domin samun albarkar amfanin gona.

A cewar sa, fiye da kashi casa’in na abincin da ake nomawa ko ake sayarwa daga kasa suke fita, don haka ne tsangayar ta baiwa kungiyar AFAN gudunmawar  kayayyaki gwaji kuma ta nuna yadda mahalarta taron za su yi amfani da su.

A nasa jawabin, Shugaban kungiyar AFAN a Jihar Jigawa, Injiniya Auwalu Garba Ibrahim, ya ce mahalarta taron zasu je yankunan su daban-daban domin ilimantar da manoma abin da suka koya a lokacin bitar.

Ya kuma godewa Jami’ar da tsangayar koyar da aikin gona saboda taimakawa kungiyar AFAN da sabbin dabarun bunkasa noma da cin ribar noma a jihar.

Mahalarta taron sun nuna jin dadin su tare da godewa jami’ar da kuma kungiyar AFAN bisa shirya bitar, wadda suka ce sun karu sosai a fannin inganta noma.

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara