Labarai
Kotu Ta Yankewa Wani Mutum Hukuncin Zaman Gidan Yari Na Watanni 2 Bisa Satar Doya
Kotun Majistare da ke Gwagwalada a babban birnin tarayya Abuja, ta yanke wa wani mutum mai suna Isah Sani hukuncin daurin watanni biyu a gidan yari bisa samunsa da laifin satar doya da kudinta ya kai Naira dubu dari da arba’in da hudu.
Mutumin wanda ya nemi kotu ta mishi sassauci, an yanke masa hukuncin ne kan aikata laifuka da sata.
Alkalin kotun Jacinta Okeke, ta yanke wa Sani hukuncin zaman gidan yari na watanni biyu ko kuma yin aiki a kasuwar Gwagwalada.
Ta kuma gargade shi da ya guji aikata laifuka.
Tun da farko, lauya mai shigar da kara, Abdullahi Tanko, ya shaida wa kotun cewa mai shigar da kara, Liasu Saidu, na kauyen Ukara, ya kai rahoton lamarin ofishin ‘yansanda a ranar 9 ga watan Mayu.
Tanko ya ce wanda aka yankewa laifin ya kutsa kai cikin gonar wanda ya kai karar ya tuge masa doyar da ya shuka wadda kudinta ya kai Naira 144,000.
A cewarsa laifin ya sabawa sashe na 348 da na 287 na kundin laifuka.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
