Connect with us

Labarai

Karamar Hukumar Kauru Ta Raba Kayayyakin Abinci Na Miliyoyin Naira Ga Marasa Galihu

Published

on

A kokarin da take na inganta rayuwar al’umma, Majalisar Karamar Hukumar Kauru da ke Jihar Kaduna ta raba kayayyakin abinci na  miliyoyin Naira ga marasa galihu.

A cikin wata sanarwa da jami’in yada labarai na majalisar Alhaji Sani Yahaya ya fitar, ya ce an shirya wannan karamcin ne da nufin rage matsalolin tattalin arziki da mazauna yankin ke fuskanta sakamakon cire tallafin man fetur da aka yi a baya-bayan nan, wanda ya haifar da tashin gwauron zabin farashin kayayyakin abinci.

Shugaban karamar hukumar Alhaji Bashir Tanko Dawaki ne ya kaddamar da rabon kayayyakin a hukumance a Kauru.

Ya bayyana cewa an zabo wadanda suka ci gajiyar shirin ne daga sassan kananan hukumomin domin tabbatar da ganin wadanda suka cancanta ne suka amfana, tare da yin rabon bisa adalci.

Alhaji Bashir Tanko Dawaki ya bukaci masu ruwa da tsaki wajen rabon kayan abinci da su tabbatar da adalci, don ganin tallafin ya isa ga wadanda suka cancanta a gundumomi  goma sha daya da ke yankin.

Ya kuma yabawa gwamnatin jihar karkashin jagorancin Gwamna Uba Sani, bisa kokarin da ta yi wajen bullo da shirye-shirye da ayyukan da ke da tasiri ga rayuwar aal’umma.

Shugaban ya shawarci wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da kayan abinci yadda ya kamata, ya kuma yi kira ga wadanda ba su samu ba a wannan karon da su yi hakuri, domin za a  kara wani rabon nan gaba kadan.

Wadanda suka ci gajiyar shirin sun nuna jin dadinsu ga majalisar karamar hukumar bisa wannan karamci.

Sun yi alkawarin bayar da goyon bayansu ga gwamnati mai ci, tare da yi mata addu’ar samun nasara.

An raba buhunan abinci daban daban guda 886 da suka hada da masara, gero, da dawa, inda aka bada fifiko ga mata da masu rauni a cikin al’umma.

Wannan kokarin da karamar hukumar Kauru ta yi ya jaddada kudirinta na tallafa wa marasa galihu domin rage radadin matsin rayuwa da ya addabi al’umma.

 

Yusuf Zubairu

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara