Connect with us

Labarai

Kano Tana Karfafa Shirin Rigakafi Ga Yaran da Ba Su Karbi Allura Ba

Published

on

A wani yunkuri na ƙarfafa shirin rigakafin yau da kullum, Hukumar Kula da Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Kano ta gudanar da wata ganawa ta musamman da manyan masu kula da cibiyoyin lafiya da Jami’an Rigakafi na yau da kullum daga kananan hukumomi 15 da aka gano suna da yawan yaran da ba su taba karɓar ko wace allurar rigakafi ba.

Taron wanda aka gudanar a hedikwatar hukumar da ke Na’ibawa, ya samu jagorancin Darakta Janar, Farfesa Salisu Ahmed, wanda ya sake jaddada kudirin gwamnatin jihar na tabbatar da an kai wa kowane yaro da aka bari a baya rigakafi.

Tattaunawar ta mayar da hankali ne kan sabon tsarin na rigakafin yau da kullum, wanda aka tsara domin ganowa, bibiyar su da kuma yi wa yaran da ba su taba karɓar allura ba ko kuma wadanda ba su kammala jadawalin rigakafinsu ba allurar da ta dace, musamman a al’ummomin da matsalar ta fi kamari.

Farfesa Ahmed ya bayyana cewa kawar da yankunan da ke da yawan yaran da ba a musu alluran ba na daga cikin manyan manufofin lafiyar al’umma, inda ya bukaci shugabannin cibiyoyin lafiya su tabbatar da ingancin bayanai, tsauraran sa ido a filin aiki, da kuma ƙarfafa wayar da kan al’umma domin ƙara yawan masu karɓar rigakafi.

Daya daga cikin muhimman batutuwan da aka tattauna a taron shi ne fayyace rawar da kowane mamba na tawagar kananan hukumomi zai taka, domin tabbatar da hadin kai, ɗaukar alhaki, da kuma sa ido kan yadda ake aiwatar da shirin yadda ya kamata.

Darakta Janar ya kuma bukaci mahalarta taron su nuna jajircewa da kishin aiki, su ƙarfafa tsarin kulawa da sa ido, tare da samar da sakamakon da zai nuna irin jagorancin da Jihar Kano ke da shi a fannin gyaran tsarin kula da lafiyar matakin farko.

Shirin na samun tallafi daga gidauniyar Bill & Melinda Gates ta hannun abokan hulɗa masu aiwatarwa, domin rage gibin rigakafi da kuma kare lafiyar kowane yaro a Jihar Kano.

Hukumar ta kuma jaddada cewa ci gaba da irin wannan hadin gwiwa a matakin kananan hukumomi na da matukar muhimmanci wajen cimma burin kasa na rigakafi tare da tabbatar da cewa babu wani yaro da za a bari a baya.

Khadijah Aliyu/Kano

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara