Connect with us

Labarai

Kafar United Daya Ta Kai Wasan Karshe A Gasar Europa League

Published

on

Ƙafar Manchester United guda ta kai wasan ƙarashe na gasar Zakarun Turai ta Europa League bayan da ta doke Athletic Bilbao da ci 3-0 a Sifaniya.

Da fari wasan ya nuna kamar ba zai yi wa United kyau ba, to amma bayan minta 30 sai wasan ya sauya bayan da Harry Maguire ya yi wata bajinta tare da buga ƙwallo zuwa da’irar bilbao, lamarin da ya bai wa Casemiro damar zura ƙwallon farko a wasan.

Minti uku bayan nan ne United ta ƙara samun wata damar bayan da ɗan wasan bayan Bilbao, Dani Vivian ya yi wa Rasmus Hojlund ƙeta a yadi na 18, inda bayan duba na’urar taimaka wa alƙalin wasa ta VAR, aka bai wa Vivian jan kati tare da bai wa United bugun fenareti.

Bayan da Bruno ya buga fenaretin ya kuma ci, ya ƙara ta uku kafin tafiya hutun rabin lokaci bayan da ɗan wasan Bilbao ya yi kuskure.

A mako mai zuwa ne United – wadda kofin Europa ne kawai fatanta a wannan kaka – za ta karɓi baƙunci Bilbao a filin wasa na Old Trafford.

A ɗaya wasan na Europa kuwa, Tottenham ce ta samu nasara kan Bodø/Glimt da ci 3-1 a Ingila.

Masu nazarin ƙwallon ƙafa na hasashen buga wasan ƙarshe tsakanin ƙungiyoyin Ingila, United ta Tottenham a gasar ta Europa, wani abu da aka jima ba a gani ba.

Can ma a ƙaramar gasar ta Conference League, Chelsea ta samu nasarar doke Djurgården da ci 4-1, wadda ita ma ake hasashen za ta kai wasan ƙarshe na gasar.

A mako mai zuwa ne Arsenal za ta je gidan PSG a babbar gasar Zakatun Turai ta Champions League, da nufin ɗaukar fansa kan ci 1-0 da PSG ta yi mata a Emirates.

Labarai

Labarai7 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara