Labarai
Jirgin Farko Na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasa Mai Tsarki
Alhazai Dari Uku da goma sha uku da suka fito daga jihar Kwaran Najeriya sun isa kasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin bana.
Jirgin Air Peace Air ya dauki mahajjatan ne a filin jirgin sama na Ilorin da misalin karfe goma sha daya da rabi na safe zuwa filin jiragen sama na Meddina da ke kasar ta Saudiyya.
Kaddamar da jirgin farkon ya samu halartar Amirul Hajj na jihar Sanata Yahaya Oloriegbe, da wakilin gwamnan jihar, Alhaji Lateef Jiddah, da shugaban hukumar jin dadin alhazai ta jihar Farfesa Moshood Jimba da sauran mambobin hukumar.
A jawabinsa, Amirul Hajj na jihar Sanata Yahaya Oloriegbe ya shawarci mahajjatan da su zama jakadu nagari ga jihar da Najeriya baki daya.
Ya kuma bukace su da su yi wa Shugaban kasa da Gwamnan Jihar addu’ar samun nasarar ayyukan da suka sanya a gaba.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Ilimi6 days ago
Gwamna Namadi Ya Nada Sabon Shugaban Hukumar Tsangaya Ta Jihar Jigawa
-
Labarai6 days ago
Kashim Shettima Ya Kaddamar da Majalisar Shawara ta Kasa Kan Tsaro
-
Labarai6 days ago
Shugaba Tinubu Ya Yi Ta’aziyya Ga Mele Kyari Kan Rasuwar ‘Yarsa
-
Labarai6 days ago
An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin IPMAN Da NNPCL
-
Labarai4 days ago
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi A Karamar Hukumar Gwaram
-
Labarai6 days ago
Gwamna Radda Ya Ba Da Gudunmawar Dala Dubu 10 Ga Jamhuriyar Nijar
-
Labarai4 days ago
Jam’iyyar PDP Ta Kauracewa Zaben Kananan Hukumomi A Jihar Nasarawa
-
Labarai4 days ago
Gobara: ‘Yan Majalisar Zamfara Sun Jajantawa Shugaban Majalisar