Labarai
Jirgin Farko Na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasa Mai Tsarki
Alhazai Dari Uku da goma sha uku da suka fito daga jihar Kwaran Najeriya sun isa kasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin bana.
Jirgin Air Peace Air ya dauki mahajjatan ne a filin jirgin sama na Ilorin da misalin karfe goma sha daya da rabi na safe zuwa filin jiragen sama na Meddina da ke kasar ta Saudiyya.
Kaddamar da jirgin farkon ya samu halartar Amirul Hajj na jihar Sanata Yahaya Oloriegbe, da wakilin gwamnan jihar, Alhaji Lateef Jiddah, da shugaban hukumar jin dadin alhazai ta jihar Farfesa Moshood Jimba da sauran mambobin hukumar.
A jawabinsa, Amirul Hajj na jihar Sanata Yahaya Oloriegbe ya shawarci mahajjatan da su zama jakadu nagari ga jihar da Najeriya baki daya.
Ya kuma bukace su da su yi wa Shugaban kasa da Gwamnan Jihar addu’ar samun nasarar ayyukan da suka sanya a gaba.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
