Labarai
Jirgin Farko Na Alhazan Jihar Jigawa Zai Tashi A Yau Litinin
Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Jigawa ta ce za a fara jigilar maniyyata na bana daga ranar Litinin 3 ga watan Yuni 2024.
Babban Daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka ga wakilinmu Usman Mohammed Zaria a Dutse.
Ya bayyana cewa Alhazan za su tashi ne daga filin jirgin Nuhu Muhammadu Sunusi zuwa kasar Saudiyya a cikin jirgin Max Air.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya yi nuni da cewa hukumar ta kammala shirye-shiryen jigilar Alhazai zuwa kasa mai tsarki, inda a halin yanzu an samar da takardun izinin shiga kasar ta Saudiyya wato biza ga Alhazan jihar.
Ya kuma bukaci Alhazai da su rika karbar umarni daga jami’an shiyyarsu na kananan hukumomi.
Ya bayyana cewa hukumar ta tsara dabarun tabbatar da tsaron Alhazanta a yayin da suke sansanin Alhazai da ke fanisau.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya kuma gargadi maniyyatan da su guji daukar abubuwan da aka haramta a cikin jakunkunansu.
Ya yi nuni da cewa, wajibi ne Alhazan su guji daukar abubuwa da suka hada da wukake da almakashi da makamantansu a jakunkunansu.
Babban Daraktan ya ce hukumar ta kuma gargadi Alhazan jihar kan daukar turare a cikin gwangwani, musamman dan feshi.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
