Connect with us

Ilimi

Jihar Jigawa Ta Amince da Naira Biliyan 3.5 a Matsayin Kudaden Tallafin UBEC 2025

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin jihar Jigawa ta amince da fitar da Naira Biliyan 3 a matsayin  tallafin hadin gwiwa na kowace shekara  domin inganta ilimi a matakin farko, wato UBEC 2025 Matching Grant.

A wata sanarwa da Kwamishinan  Yada Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na Jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya fitar ya bayyana cewa za a yi amfani da kudaden ne wajen gina sabbin azuzuwa, gyare-gyare, haka rijiyoyin burtsatse da kuma samar da kayan koyo da koyarwa ga dalibai da malamai.

Ya ce, majalisar ta kuma amince da sama da Naira Miliyan 289 domin gina sabbin ofisoshin gudanarwa da gyare-gyare a kananan hukumomi 9 na jihar.

A cewarsa, za a yi amfani da kudaden ne wajen gina ofisoshin gudanarwa a GDASS Imam Hassan Kafin Hausa, gina rukuni 8 na wuraren ba-haya a wasu makarantun IEB da aka zaɓa, da kuma ayyukan gyare-gyare a GGASS Danzomo da SAIS Hadejia.

Ya ce waɗannan matakai na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen inganta ilimi da habaka ƙwarewar ɗan adam.

Sagir Musa Ahmed ya bayyana cewa makarantun da za a yi wa ayyukan sun haɗa da GDASS Imam Hassan a Karamar Hukumar Kafin Hausa, GDASS Danzomo a Karamar Hukumar Sule Tankarkar, SSIS Hadejia a Karamar Hukumar Hadejia, da GDASS Tarubu a Karamar Hukumar Kirikasamma.

Sauran sun haɗa da GDASS Sani Ayu a Karamar Hukumar Gumel, GDASS Shuarin a Karamar Hukumar Kiyawa,
GDASS Kaugama a Karamar Hukumar Kaugama, GDASS Kwaimawa a Karamar Hukumar Dutse, da GDASS Harbo Tsohuwa a Karamar Hukumar Miga.

Kwamishinan ya ƙara da cewa majalisar ta kuma amince da kwangilar sama da Naira Biliyan 1 domin gyaran tsofaffin gine-ginen cibiyoyin kiwon lafiya 30 da aka farfaɗo da su a bara.

Game da batun haɗin gwiwa don rage talauci kuwa, Sagir ya bayyana cewa majalisar ta amince da kashe Baira Miliyan 600 domin sabunta da faɗaɗa rajistar jin daɗin jama’a ta jihar ga Hukumar Jigawa Operation Coordination Unit da Hukumar CARES ta jihar (SCCU), kasancewar hakan shi ne sharadin shiga shirin Bankin Duniya na tallafin jin daɗin jama’a da rage talauci a jihohi.

 

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara