Connect with us

Labarai

Jagoran Mulkin Sojin Chadi Ya Bayyana Aniyar Takara Gabanin Zabe

Published

on

Jagoran gwamnatin sojin Chadi, Mahamat Idriss Deby Itno ya bayyana aniyarsa ta yin takara a zaben shugaban kasar mai zuwa, wanda aka tsara za a yi a ranar 6 ga wata Mayun wannan shekarar, kwanaki 3 kacal bayan da aka kashe babban abokin hamayyarsa a wani yanayi mai sarkakiya.

Deby Itno ya dare karagar mulkin Chadi ne a shekarar 2021, bayan mutuwar mahaifinsa Idriss Deby Itno a yayin da ya ke jagorantar yaki da ‘yan tawaye, bayan sama da shekaru 30 a kan mukamin shugaban kasar da ke yankin Sahel.

 

Mahamat Idriss Deby Itno, ya bayyana a wani jawabi da ya gabatar wa al’ummar kasar cewa zai yi takarar shugabancin kasar a karkashin gamayyar da gwamnati ta hada.

 

A shekarar 2021 ce aka nada Deby a matsayin jagoraan gwamnatin soji, kuma a lokacin ne ya yi alkawarin mika mulki ga farar hula a cikin watanni 18.

 

Amma Deby ya tsawaita wannan wa’adi da karin shekaru 2, kuma gwamnatinsa ta yi amfani da karfi fiye da kima wajen murkushe masu zanga-zangar adawa da matakin nasa a watan Oktoban shekarar 2022.

 

A ranar Talatar da ta gabata ce gwamnatin sojin Chadi ta sanar da cewa a ranar 6 ga watan Mayu za ta gudanar da babban zaben kasar.

 

Masu lura da al’amura na cewa Deby mai shekaru 39 yana da yakinin lashe zabe, duba da cewa an kashe babban abokin hamayyarsa, kuma dan uwansa, Yaya Dillo Djerou, kuma ga shi mahukunta sun murkushe sauran ‘yan adawa.

Labarai

Labarai3 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai23 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara