Labarai
Isra’ila Ta Ce Za Ta Lalata Birnin Gaza Idan Hamas Ba Ta Amincewa Da Sharuddanta Ba
Ministan tsaron Isra’ila, Israel Katz, ya bayyana cewa za a lalata birnin Gaza gaba ɗaya idan kungiyar Hamas ta ƙi miƙa makamai da kuma sakin dukkan fursunonin da take riƙe da su.
Wannan furuci nasa ya zo ne bayan majalisar ministocin Isra’ila ta amince da sabon shirin kai farmaki a birnin Gaza duk da suka da adawa daga ƙasashen duniya da ma cikin gida.
A cikin sanarwar da ya fitar a shafinsa na X, Katz ya ce: “Idan har Hamas ba ta amince da sharuɗɗan Isra’ila na kawo ƙarshen yaƙi a Gaza ba, musamman sakin dukkan fursunoni Isra’ila da kuma miƙa makamai ba, toh babban birnin Gaza zai zama kamar birnin Rafah da Beit Hanoun,” in ji shi.
Wadannan garuruwa biyu da ya ambato dai sun ruguje sakamakon hare-haren da sojojin Isra’ila suka kai a baya.
-
Labarai4 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai5 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai1 day agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai2 days agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
-
Labarai4 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
