Connect with us

Labarai

IAR da NAERLS Sun Shirya Taron Tattaunawa Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Noma Dawa A Najeriya

Published

on

 

Cibiyar Bincike Kan Harkar Noma (IAR) tare da hadin gwiwar Hukumar Yada Sakamakon Bincike da Wayar da Kan Manoma ta Kasa (NAERLS), Jami’ar Ahmadu Bello Zaria, sun shirya taron kwana guda a Kaduna domin masu ruwa da tsaki kan aikin bunkasa noman dawa a Najeriya.

 

Taken taron shi ne: “Gabatarwa da Tattaunawa Kan Amfanin Sabbin Nau’ikan Dawa Masu Jure Sauyin Yanayi Domin Rage Talauci da Inganta Abinci a Najeriya.”

 

Daga cikin manyan abokan aikin akwai Kungiyar Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afrika (ECOWAS), Kungiyar Manoman Dawa da Masara ta Najeriya, da Tarayyar Turai (EU), da sauransu.

A jawabin sa, Mataimakin Daraktan NAERLS, Farfesa Muhammad Musa Jaliya, ya ce babban burin taron shi ne tabbatar da dorewar sabon tsarin nomar dawa a Najeriya.

 

“Ba ma so mu gudanar da aikin kawai ya ƙare ba tare da dorewa ba. Babban dalilin wannan taro shi ne samar da mafita don dorewar aikin. Manoma sun rungumi aikin, kuma sun samu sauyi ta fuskar iri na dawa masu inganci da fa’ida,” in ji shi.

 

A tattauna da Radio Nigeria Kaduna, Shugaban Kungiyar Manoman Dawa ta Kasa, Dr. Adamu Yusuf, ya jaddada muhimmancin Najeriya a matsayin jagora a noman dawa a duniya. Ya ce ya kamata ‘yan Najeriya su ci gaba da addu’a da kokari domin kasar ta ci gaba da rike matsayinta a matsayin kasa ta daya ko ta biyu wajen noman dawa a duniya.

 

Ita ma a nata jawabin, Farfesa Aisha AbdulKadir daga IAR, ABU Zaria, ta bayyana cewa sun samu nasarar gabatar da sabbin nau’ikan iri na dawa a Najeriya.

 

“Muna son ganin mutane sun rungumi wadannan nau’ikan iri, muna kuma neman jin ra’ayoyin masu ruwa da tsaki da manoma don mu kara samun ci gaba,” in ji ta.

 

Wakilin ECOWAS a taron, Farfesa Mamman Saleh, ya bayyana cewa ECOWAS ta kuduri aniyar inganta rayuwar al’ummomin yankin ta hanyar bunkasa tattalin arziki da ayyukan noma.

“ECOWAS ta kafa hukumar kula da harkokin noma da albarkatun kasa domin tallafa wa ayyukan noman dawa na musamman, da nufin samar da ayyukan yi ga matasa da inganta gina kasa, da kuma dawo da filayen noma da suka lalace,” in ji shi.

 

Masu halarta taron sun fito ne daga Jihar Kaduna da sassa daban-daban da ke da alaka da harkar noman dawa.

 

Cov/Adamu Yusuf

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara