Connect with us

Ilimi

Hukumar Zakka da Waƙafi ta Jihar Zamfara…

Published

on

Hukumar Zakka da Waƙafi ta Jihar Zamfara

Fata Ga Marasa Galihu Da Kawo Canji A Rayuwar Jama’a

Daga Abdullahi Musa

A ‘yan makonnin da suka gabata ne Hukumar Zakka da Waƙafi ta jihar Zamfara ƙarƙashin jagorancin Sheikh Umar Ahmad Kanoma, ta bullo da wasu sabbin hanyoyi da tsare-tsaren taimaka wa wajen canja rayuwar al’umma da kyautata jin dadin da kuma zamantakewarsu.

Hukumar ta ƙarfafa hanyoyin da aka san ta su na jajircewa wajen yi wa al’umma hidima cikin tausayi da adalci, Hukumar ta samu gagarumin ci gaba a ayyukanta na rage radadin talauci da ƙarfafa wa marasa galihu a lokacin Azumin watan Ramadan da ya gabata.

Bisa kulawar sakataren zartaswa, Habib Balarabe Muhammad, Hukumar ta samu gagarumar nasara wajen tallafa wa mabuƙata da marasa galihu.

Hukumar ta Kai ɗaukin gaggawa ga mata masu fama da matsalar shaye-shayen miyagun ƙwayoyi da haifar masu da fata a zukatansu, ta hanyar shirya masu tarukan fadakarwa da nufin kyautata rayuwarsu.

Baya ga samar wa mata da matasa marasa galihu hanyoyin dogaro da kai, Hukumar ta tallafa masu da mahimman kayayyakin koyon sana’a da haɓaka ƙwarewa a tsakaninsu. Wannan tsarin jin kai yana nuna sadaukarwar Hukumar don jindadin marasa galihu.

A cikin watan Ramadan, Hukumar ta kara kaimi, inda ta tallafa wa mutane sama da 40,000 a fadin jihar Zamfara da kayan abinci da taimakon kuɗi.

Bugu da ƙari, Hukumar ta samar da gaɓoɓin roba kyauta ga mutanen da rasa gaɓoɓinsu sakamako hattsura ko ayyukan ‘yan ta’adda da taimaka wa mata masu matsalar cutar yoyon fitsari (VVF). Hakan ya jaddada himmar Hukumar wajen samun damar kiwon lafiya da nufin inganta rayuwar marasa galihu.

Ta hanyar haɗin gwiwa da ƙungiyoyi jin kai kamar; Bright Futures Serious da Organised Crime Prevention Project (SOC), Hukumar ta samar da tsare-tsare don rigakafi da kuma tsarin tallafi, tabbatar da samari masu aikata laifuka sun sami jagoranci na gari a rayuwarsu da nufin ƙarfafa su don kawar da aikata miyagun laifuka a tsakanin al’umma a jihar.

Bayan Eid al-Fitr, Hukumar ta kasance mai himma, tare da yin alƙawarin shigar ɗaruruwan mutane a cikin shirye-shiryen gina rayuwarsu da dabarun haɓaka fasaha. Wannan tsarin sa ido yana nuna sadaukarwarsu ga ƙarfafawa ta dogon lokaci da nufin samar da mafita mai dorewa ga al’umma.

Nasarorin da Hukumar ke samu sun nuna muhimmancin samar da kyakkyawan tsari daa irin tasirin da yake da shi. Tun daga yunkurin agajin gaggawa zuwa shirye-shiryen karfafawa na dogon lokaci, kowane aiki yana kunshe da ka’idojin hadin gwiwa da jin kai da ke cikin Zakka.

Hukumar ta yi alƙawarin kiyaye ƙa’idodin aiki, haɓaka haɗin gwiwa, da bullo da sabbin hanyoyi don magance talauci da kuma fuskantar ƙalubalen tattalin arziki yadda ya kamata.

Tare da jajircewa wajen yi wa al’umma hidima bisa tsarin addinin Musulunci, Hukumar Zakka da Waƙafi ta jihar Zamfara ta tsaya tsayin daka a matsayin wata fitilar da ke haskaka rayuwar marasa galihu da kuma samar masu da fata a rayuwa.

Fassara/Wababe/ Caliphate Times

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara