Labarai
Hukumar JSPCACC Ta Kwato Kudaden Gwamnati Sama Da Naira Miliyan 300
Gwamnatin jihar Jigawa ta nemi hadin kan al’umma don gina kasa bisa gaskiya da rikon amana, tare da kaucewa cin hanci da rashawa ba.

Gwamna Umar Namadi ya yi wannan kiran a lokacin bude taron wayar da kan jama’a na yini 3 da Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Jigawa (JSPCACC) ta shirya a Dutse.

Malam Umar Namadi ya bayyana cewa, taron na da nufin wayar da kan manyan jami’an gwamnati kan ayyukan hukumar da sauran batutuwan da suka shafi hakan.
“Wannan shiri yana da matukar muhimmanci idan aka yi la’akari da yadda gwamnati ta jajirce wajen ci gaba da inganta dukkan ka’idojin gudanar da mulki.”


Gwamna Namadi ya ce, cin hanci da rashawa al’ada ce da ta yadu da ke wargaza al’umma, da cibiyoyin gwamnati.
Ya yi nuni da cewa, shugabanci nagari wanda ya hada da kaucewa rikon sakainar kashi da kin bin son zuciya, sgi ne hanya daya tilo ta yaki da talauci, da ci gaban al’umma cikin sauri, da samar da sauye-sauye masu kyau a cikin al’umma.


Ya ce, ingantaccen tsarin mulki, wanda ke tattare da rikon amana da gaskiya, shi ne tabbacin samun nasara a yakin da ake da talauci, da saurin ci gaban tattalin arziki, da sauye-sauye a tsakanin al’umma.
Namadi wanda ya bayyana gagarumin ci gaban da hukumar ta samu tun bayan kafa ta a shekarar 2022, ya bayyana cewa, ta kwato sama da naira miliyan 300 na kudaden gwamnati, tare da warware kusan rabin korafe-korafe 200 da aka samu, kuma a halin yanzu ta gurfanar da wasu kararraki 16.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
