Labarai
Hukumar Alhazai Ta Kasa Ta Sanar Da Kudin Aikin Hajjin Bana
Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da kudin aikin Hajjin shekarar 2025.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun
Mataimakiyar Daraktan Watsa Labarai ta hukumar, Fatima Sanda Usara.
Ta ce “Hukumar aikin Hajji ta kasa (NAHCON), a karkashin jagorancin shugabanta, Farfesa Abdullahi Saleh Usman na farin cikin sanar da kudin aikin Hajjin shekarar 2025”.
Ta ce an sanar da kudin kujerar na bana ne bayan amincewar ofishin mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima.
Ta kara da cewa “Hakika Shugaban Hukumar NAHCON da tawagarsa tare da hadin guiwar wakilin fadar shugaban kasa, Malam Ameen Amshi, wanda shi ne mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan ayyuka na musamman, sun yi kokari matuka wajen ganin an biya kudin aikin Hajji daidai da yadda aka biya a bara.
“Maniyyata aikin Hajjin 2025 daga shiyyar Borno da Adamawa, za su Naira miliyan 8,327,125.59 (miliyan takwas, da dubu dari uku da ashirin da bakwai, da dari daya da ashirin da biyar da kwabo hamsin da tara).
“Hakazalika, maniyyata daga jihohin Kudu za su biya Naira miliyan 8, 784, 085.59 (miliyan takwas, da dubu dari bakwai da tamanin da hudu, da Naira tamanin da biyar Naira kobo hamsin da tara).
“Alhazan da suka fito daga shiyyar Arewa kuma za su biya Naira 8, 457,685.59 (miliyan takwas, da dubu dari hudu da hamsin da bakwai, da dari shida da tamanin da biyar da kwabo hamsin da tara).”
Fatima Usara ya ce Farfesa Saleh ya yaba wa daukacin tawagar, inda ya bayyana kudin aikin Hajjin a matsayin wani babban hadin gwiwa da duk masu ruwa da tsaki.
Ya yaba da goyon bayan fadar shugaban kasa da kungiyar sakatarorin gudanarwa na jihohi.
Shugaban ya bukaci maniyyatan da suke son zuwa aikin Hajji da su lura da ka’idoji hukumar da na kasar Saudiyya, tare da jaddada mahimmancin biyan kudi da wuri da kuma yin rajista a kan lokaci don guje wa matsaloli.#Hajj2024
Safiyah Abdulkadir
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
