Labarai
Hukumar Alhazai Ta Jihar Kwara Ta Jajantawa Iyalan Alhazan Da Suka Rasu
Hukumar Alhazai ta jihar Kwara ta jajantawa iyalan wasu alhazai biyu da suka rasu a birnin Madina na kasar Saudiyya.
A cikin wata sanarwa da sakataren zartarwa na hukumar jin dadin alhazai ta jihar Alhaji Abdulkadir Abdulsalam Ya fitar, ya ce Saliu Mohammed, wanda ya zo a sahu na 3 na alhazan har, ya rasu ne a sashin kula da marasa lafiya na wani asibitin gwamnati da ke Madina.
Ya ce Hajiya Hawawu Mohammed da ke cikin rukuni na 9 kuwa, ta rasu ne biyo bayan fadowa daga saman benen masaukinsu da ke Madina.
Alhaji Abdulsalam ya ce hukumar alhazai na cike da alhinin wannan lamarin, ta kuma mika ta’aziyya ga iyalansu tare da yi musu addu’ar Allah ya jikan su da Aljannar Firdausi.
Ali Muhammad Rabi’u
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai15 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
