Connect with us

Labarai

Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Fara Biyan Rarar Kudade Ga Alhazan 2023

Published

on

 

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna ta fara biyan Naira 61,080 ga mahajjata 6,239 kowannensu,  da suka yi aikin Hajji daga jihar a shekarar 2023.

Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Yunusa Mohammed Abdullahi ya sanya wa hannu, ta bayyana cewa kowane mahajjaci zai karbi kudi naira 61,080, kuma za a shigar da wadannan kudade kai tsaye cikin asusun ajiyar maniyyatan da abin ya shafa.

Hukumar ta karbi wadannan kudaden ne daga hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON)”. Inji sanarwar.

NAHCON ta bayyana  cewa an mayar da kudaden ne sakamakon katsewar wutar lantarki a lokacin da Alhazai suka yi zaman Muna, lamarin da ya shafi na’urorin sanyaya daki, da kuma kawo cikas ga mahajjata”.

“Za mu yi duk mai yiwuwa don tabbatar da ganin an biya mahajjatan ta asusun  bankinsu don gujewa matsala,” inji Shugaban Hukumar, Malam Salihu S. Abubakar, a wani taro da jami’an  Alhazai na kananan hukumomin.

Sanarwar ta yi kira ga Alhazan da abin ya shafa da har yanzu ba su mika bayanansu ba da su tuntubi jami’an karamar hukumarsu domin a tantance su .

Abubuwan da ake buƙata don tantancewar sun haɗa da fasfo na tafiya da bayanan asusun banki.

Shugaban Hukumar, Malam Salihu S. Abubakar, ya bukaci jami’an hukumar da su tabbatar da bin ka’idoji bisa  gaskiya da  amana.

 

Adamu Yusuf

Labarai

Labarai15 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai2 days ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara