Labarai
Hukumar Alhazai Ta Jihar Kaduna Ta Fara Biyan Rarar Kudade Ga Alhazan 2023
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kaduna ta fara biyan Naira 61,080 ga mahajjata 6,239 kowannensu, da suka yi aikin Hajji daga jihar a shekarar 2023.
Wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na hukumar Yunusa Mohammed Abdullahi ya sanya wa hannu, ta bayyana cewa kowane mahajjaci zai karbi kudi naira 61,080, kuma za a shigar da wadannan kudade kai tsaye cikin asusun ajiyar maniyyatan da abin ya shafa.
“Hukumar ta karbi wadannan kudaden ne daga hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON)”. Inji sanarwar.
“NAHCON ta bayyana cewa an mayar da kudaden ne sakamakon katsewar wutar lantarki a lokacin da Alhazai suka yi zaman Muna, lamarin da ya shafi na’urorin sanyaya daki, da kuma kawo cikas ga mahajjata”.
“Za mu yi duk mai yiwuwa don tabbatar da ganin an biya mahajjatan ta asusun bankinsu don gujewa matsala,” inji Shugaban Hukumar, Malam Salihu S. Abubakar, a wani taro da jami’an Alhazai na kananan hukumomin.
Sanarwar ta yi kira ga Alhazan da abin ya shafa da har yanzu ba su mika bayanansu ba da su tuntubi jami’an karamar hukumarsu domin a tantance su .
Abubuwan da ake buƙata don tantancewar sun haɗa da fasfo na tafiya da bayanan asusun banki.
Shugaban Hukumar, Malam Salihu S. Abubakar, ya bukaci jami’an hukumar da su tabbatar da bin ka’idoji bisa gaskiya da amana.
Adamu Yusuf
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai15 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
