Labarai
Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Za Ta Karfafa Dangantaka Da NAFDAC
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa zata kara karfafa dankon zumunta da Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Kasa NAFDAC.
Darakta Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ya bayyana haka a lokacin da mahukunta hukumar NAFDAC suka ziyarce shi a ofishin sa dake Dutse babban birnin jihar.
Ya bayyana farin cikinsa da ziyayar, inda ya jaddada bukatar aiki tare domin cimma dukkan nasarar da ake bukata a tsakanin hukumomin biyu.
Da yake bayani dangane da shirin da hukumar alhazan take yi, Labbo yace dukkanin shirye-shirye sunyi nisa na rigistar kujerun aikin hajji shekarar 2026.
Yana mai cewar, hukumar NAFDAC tana cikin masu ruwa da tsaki na hukumar jin dadin alhazan jihar.
Alhaji Ahmed Labbo, yayi nuni da cewar akowane lokaci za’a iya bukatar tattauna muhimman bayanai na shirye-shiryen aikin hajji domin bada ta su gudunmuwar.
Tun farko a jawabin sa, sabon Shugaban hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa NAFDAC a jihar jigawa, Alhaji Mansur Muhammad yace makasudin ziyarar shi ne domin gabatarwa gami da neman goyan bayan hukumar jin dadin alhazan ta jihar.
Ya kara da cewar, hukumar tana daga cikin hukumomi dake aiki tare da hukumar NAFDAC musamman a lokacin fara jigilar maniyyata.
Mansur Muhammad yace za su ci gaba da bai wa hukumar cikakken hadin kai da goyan baya a duk lokacin da bukatar hakan ta taso.
Usman Mohammed Zaria
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
