Connect with us

Labarai

Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Ta Yi Tanadi Na Musamman Ga Alhazanta A Mina

Published

on

Alhazan Jihar Jigawa sun fara ayyukan hajji cike da kwarin gwiwa yayin da aka kaisu Mina daga birnin Makkah, inda za su wuce zuwa Dutsen Arafat domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.

Aikin hajji na farawa ne daga ranar 8 zuwa 13 ga watan Dhul Hajj a duk shekara, inda ake daukar alhazai zuwa sansanin Mina sannan su wuce zuwa Arafat, zuwa Muzdalifa, sannan Jamarat (Jamratul Akbah), kafin su dawo Makkah inda za su kammala da Dawafi.

Yawancin Alhazan da suka zanta da Rediyon Najeriya sun bayyana cewa, duk da wahalhalun da ke tattare da aikin hajji, sun kuduri aniyar gudanar da hajjin lafiya kuma cikin nasara.

Wasu daga cikin Alhazan daga kananan hukumomin Jahun da Kiyawa, Hajiya Maijidda Abdulhamid da Alhaji Mohammed Abdullahi Idris sun bayyana cewa tsoron Allah da kaunarsa ke basu kwarin gwiwar jure wahalhalun aikin hajji, kasancewar Allah Ya bada tabbacin karbar dukkan addu’o’i, don haka wajibi ne su jure domin babu wani alheri da ke zuwa cikin sauki.

Wani Alhaji daga Dutse, Murtala Sani Lama, ya bayyana cewa aikin hajji yana daga cikin ginshikan Musulunci, kuma kowanne musulmi mai hali yana da hakkin gudanar da shi. Ya kara da cewa a cikin Alkur’ani an bayyana cewa duk wata bukata da Alhaji ya roka za a amsa masa.

Ya kara da cewa wannan tabbacin kadai yana isar masa da kwanciyar hankali wajen shan wahalhalun aikin hajji komai yadda suka kasance.

 

Alhazan sun bayyana ra’ayin cewa kasancewar aikin hajji kira ne daga Allah kuma su baƙinsa ne na musamman, ba wani dogon tafiya ko zafi ko yawan mutane da zai hana su gudanar da ibada.

A cewar koyarwar Musulunci, duk wanda ya gudanar da aikin hajji yadda ya kamata, Allah yana gafarta masa dukkan zunubansa kuma yana bashi sabuwar dama kamar yadda aka haifi sabon jariri.

Haka kuma, a wata hira da Rediyon Najeriya, Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ya ce dukkan abubuwan da suka wajaba domin jin dadin alhazan jihar an tanade su.

An sanya ma tantin Alhazai  na’urar sanyaya daki (air condition), tare da katifa da filo da kuma bargo ga kowane Alhaji. Kuma saboda zafin rana, mun saka firijin na ruwa tsakanin tantuna domin rage hatsarin kamuwa da matsanancin kishi.”

Labbo ya kara da cewa Alhazai za su rika samun abinci sau uku a rana tare da ruwan sha, da ‘ya’yan itatuwa da kuma lemun kwalba.

Ya shawarci Alhazai da su sanya tsoron Allah a zukatansu, yana mai cewa wannan ne mataki na farko na samun hajji mai kyau da tsari.

 

Usman Mohammed Zaria

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara