Connect with us

Labarai

Gwamnatin Zamfara ta Bada Babura 10 ga ‘Yan Sanda a Jihar Domin Inganta Tsaro

Published

on

Daga Aminu Dalhatu 

Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayar da sabbin babura guda goma domin ayyukan tsaro ga Ofishin ’Yan Sanda na Gusau ta Tsakiya da nufin ƙarfafa sintiri da inganta tsaro a cikin babban birnin jihar.

An mika baburan ga DPO na ofishin ‘Yan Sanda da ke Gusau ta Tsakiya, CSP Abubakar Sani Muhammad, ta hannun Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Abubakar Mohammad Nakwada.

Wata sanarwa da Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai a Ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar, Sulaiman Ahmad Tudu, ya fitar, ta bayyana cewa Sakataren Gwamnatin ya samu wakilcin Babban Sakataren Harkokin Majalisar Zartarwa Dakta Abubakar Mohammad Gusau.

Malam Nakwada ya bayyana cewa an bayar da baburan ne domin inganta ayyukan ’yan sanda, musamman a wuraren da ba su da sauƙin shiga da motocin sintiri.

Ya kuma ƙara da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da tallafa wa Ofishin ‘Yan Sandan ta hanyar samar da man fetur da za su rika amfani da shi a ababen hawansu domin tabbatar da ingantaccen aiki da dorewar hidimar tsaro.

A cewarsa, wannan tallafi na daga cikin ƙudirin gwamnatin Gwamna Dauda Lawal na yaƙi da dukkan nau’ikan ayyukan ta’addanci da kuma ƙarfafa tsaro a fadin Jihar Zamfara.

Da yake karɓar Baburan a madadin Rundunar ’Yan Sanda ta Najeriya, DPO CSP Abubakar Sani Mohammad ya nuna godiyarsa ga gwamnatin jihar, inda ya ce Baburan za su ƙara wa sashen ƙarfi wajen tinkarar masu aikata laifuka da ke amfani da wurare masu wahalar shiga wajen aikata ayyukan ta’addanci.

Ya yabawa Gwamna Dauda Lawal bisa ci gaba da ba hukumomin tsaro tallafi, tare da tabbatar da kara jaddada cewa za su ci gaba da sauke nauyin da aka dora musu na kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

A wani labari mai nasaba da hakan, gwamnatin jihar na ci gaba da gyarawa da sake fasalin Ofishin ’Yan Sanda na Gusau ta Tsakiya da kuma Hedikwatar Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Zamfara, akan kudi kuɗaɗe kimanin Naira Miliyan 726 da dubu 900 na ofishin Gusau ta Tsakiya, da kuma Naira biliyan 1 da miliyan 400 a hedikwatar.

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara