Labarai
Gwamnatin Zamfara ta Bada Babura 10 ga ‘Yan Sanda a Jihar Domin Inganta Tsaro
Daga Aminu Dalhatu
Gwamnatin Jihar Zamfara ta bayar da sabbin babura guda goma domin ayyukan tsaro ga Ofishin ’Yan Sanda na Gusau ta Tsakiya da nufin ƙarfafa sintiri da inganta tsaro a cikin babban birnin jihar.
An mika baburan ga DPO na ofishin ‘Yan Sanda da ke Gusau ta Tsakiya, CSP Abubakar Sani Muhammad, ta hannun Sakataren Gwamnatin Jihar, Malam Abubakar Mohammad Nakwada.

Wata sanarwa da Babban Mataimaki na Musamman kan Harkokin Yaɗa Labarai a Ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar, Sulaiman Ahmad Tudu, ya fitar, ta bayyana cewa Sakataren Gwamnatin ya samu wakilcin Babban Sakataren Harkokin Majalisar Zartarwa Dakta Abubakar Mohammad Gusau.
Malam Nakwada ya bayyana cewa an bayar da baburan ne domin inganta ayyukan ’yan sanda, musamman a wuraren da ba su da sauƙin shiga da motocin sintiri.

Ya kuma ƙara da cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da tallafa wa Ofishin ‘Yan Sandan ta hanyar samar da man fetur da za su rika amfani da shi a ababen hawansu domin tabbatar da ingantaccen aiki da dorewar hidimar tsaro.
A cewarsa, wannan tallafi na daga cikin ƙudirin gwamnatin Gwamna Dauda Lawal na yaƙi da dukkan nau’ikan ayyukan ta’addanci da kuma ƙarfafa tsaro a fadin Jihar Zamfara.

Da yake karɓar Baburan a madadin Rundunar ’Yan Sanda ta Najeriya, DPO CSP Abubakar Sani Mohammad ya nuna godiyarsa ga gwamnatin jihar, inda ya ce Baburan za su ƙara wa sashen ƙarfi wajen tinkarar masu aikata laifuka da ke amfani da wurare masu wahalar shiga wajen aikata ayyukan ta’addanci.
Ya yabawa Gwamna Dauda Lawal bisa ci gaba da ba hukumomin tsaro tallafi, tare da tabbatar da kara jaddada cewa za su ci gaba da sauke nauyin da aka dora musu na kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
A wani labari mai nasaba da hakan, gwamnatin jihar na ci gaba da gyarawa da sake fasalin Ofishin ’Yan Sanda na Gusau ta Tsakiya da kuma Hedikwatar Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Zamfara, akan kudi kuɗaɗe kimanin Naira Miliyan 726 da dubu 900 na ofishin Gusau ta Tsakiya, da kuma Naira biliyan 1 da miliyan 400 a hedikwatar.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
