Kasuwanci
Gwamnatin Kano Zata Kashe Naira Miliyan Dubu 51 Don Aiwatar Da Ayukka
Majalisar zartaswar jihar Kano ta amince da kashe Naira biliyan 51.5 wanda ba a taba ganin irinsa ba, domin muhimman ababen more rayuwa da ayyukan yi wa al’umma hidima a fadin jihar, a wani bangare na tsare-tsare na gwamnatin na bunkasa zamantakewa da tattalin arziki.
Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar bayan taron majalisar zartarwa karo na 27 da aka gudanar a gidan gwamnatin Kano.
A cewar sanarwar, majalisar ta ba da haske ga manyan ayyuka da yawa, da suka hada da manyan gyare-gyaren hanyoyi, shigar da tsarin zirga-zirga, fadada gine-ginen jama’a, da inganta wutar lantarki.
Wani abin lura a cikin amincewar akwai fitar da naira biliyan 5.4 domin gyaran tituna da kwalta da suka tashi daga gidan Mumbayya zuwa Mahadar Tal’udu, Gadon Kaya, titin Yahaya Gusau, da Titin Sharada.
An kuma ware Naira biliyan 3.4 don samar da fitilun masu amfani da hasken rana a fadin birnin Kano a karkashin shirin sabunta birane.
An amince da karin wasu kudade don gina titin Miller zuwa titin Mishan da kuma gyara wasu muhimman kayayyakin aikin gwamnati da suka hada da Sashen Albarkatun Ilimi na Kano da Gidan Gwamna da ke Kaduna.
Majalisar ta kuma amince da Naira Biliyan 1.46 don ingantawa da kuma zamanantar da ma’aikatar Wutar Lantarki da Sabunta Makamashi da ke cikin Sharada.
Sanarwar ta ce “Wadannan amincewar sun nuna kudurin gwamnatin na samar da ci gaba mai dorewa a birane da kuma inganta ayyukan jama’a.”
Abdullahi Jalaluddeen/Kano
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
