Labarai
Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Raba Kayayyakin Lafiyar Mata Da Yara Kyauta
Hukumar Kula da Lafiya A Matakin Farko ta Jihar Kano (KSPHCMB) ta fara raba kayayyakin kula da mata masu juna biyu, da kananan yara kyauta a cibiyoyin kula da lafiya na matakin farko guda 106 a fadin jihar.
Wannan shiri na daga cikin alkawuran Gwamna Abba Kabir Yusuf na inganta damar samun lafiya ga mata da yara.
A yayin bikin kaddamar da rabon, Darakta Janar na KSPHCMB, Farfesa Salisu Ahmad Ibrahim, ya bayyana cewa kayayyakin za su taimaka wajen rage mace-mace da ake iya kaucewa na mata masu juna biyu da yara, ta hanyar karfafa tsarin lafiyar matakin farko a Kano.

Ya umurci Daraktocin Yankuna da Shugabannin Sassa (HODs) da su tabbatar da gaskiya da rikon amana wajen rabon kayayyakin.
Darakta Janar din ya gargadi duk wata karkatarwa ko almundahanar kayayyakin, inda ya jaddada cewa hukumar za ta sa ido sosai don tabbatar da cewa kayan sun isa ga wadanda suka dace.
Farfesa Salisu ya jinjinawa Gwamna Abba bisa cika alkawuran zabe da kuma fifita lafiyar mata da yara, tare da godewa Kwamishinan Lafiya, Dr. Labaran Abubakar Yusuf, bisa goyon baya da kyakkyawan jagoranci wajen ci gaban harkar lafiya a jihar.

Shi ma Daraktan Sashen Magunguna, Pharmacist Abdullahi Abubakar Danzabuwa, ya tabbatar da cewa kayayyakin suna da inganci sosai, kuma za a raba su bisa ka’idojin kasa da kasa na tsarin rabon magunguna da kayayyakin lafiya.
Hukumar ta KSPHCMB ta bayyana tabbacin cewa shirin zai inganta lafiyar mata da yara a jihar Kano, tare da kara tabbatar da jihar Kano a matsayin jagora a harkar lafiya a matakin farko a Najeriya.
Daga Khadijah Aliyu
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai14 hours agoHukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani
