Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Kano Ta Kaddamar Da Bincike Kan Mutuwar Dalibai Biyu A Makaranta

Published

on

Gwamnatin Jihar Kano ta kaddamar da bincike kan mutuwar ban mamaki ta wasu dalibai biyu a Kwalejin Sakandaren Gwamnati ta kwana da ke Bichi, wato Hamza Idris Tofawa da Umar Yusuf Dungurawa.

Rahotanni sun ce wasu daliban makarantar ne suka kai musu hari da wani irin l ƙarfe da ake kira “Gwale-Gwale”.

Lamarin ya tayar da ƙura inda al’umma a fadin jihar suka nemi a tabbatar da adalci game da lamarin.

Yayin da yake magana da manema labarai a madadin Kwamishinan Ilimi Dr. Ali Haruna Makoda, Babban Sakataren Ma’aikatar Ilimi, Alhaji Bashir Baffa Muhammad, ya bayyana cewa gwamnati ta ɗauki lamarin da muhimmanci kuma ba za ta yi sakaci ba wajen tabbatar da adalci.

“Gwamnatin Jihar Kano za ta gudanar da bincike busa gaskiya, da adalci. Mun sha alwashin ganin an tabbatar da adalci ga dukkan wadanda lamarin ya shafa.” Inji shi 

Ya ja hankalin dalibai da su guji ɗaukar doka a hannunsu, su riƙa kai koke-kokensu ga mahukuntan makaranta.

Babban Sakataren ya kuma miƙa ta’aziyyar gwamnati ga iyalan mamatan, tare da addu’ar samun rahama garesu.

Shugaban Sashen Makarantun Sakandare na Hukumar Gudanar da Makarantun Sakandare ta Jihar Kano, Malam Abbas Abdullahi, ya bayyana matakin da aka ɗauka a matsayin abin takaici inda ya gargadi dalibai su guji yin amfani da matsayinsu wajen cutar da wasu da kuma aikata tashin hankali.

Wani ɗan uwa ga ɗaya daga cikin mamatan, Malam Ibrahim Yusuf Dungurawa, ya bayyana irin radadin da suka shiga bayan samun labarin mutuwar ɗansu, tare da roƙon gwamnati da ta tabbatar da adalci.

Haka zalika, mahaifin ɗaya daga cikin daliban da suka rasu, Malam Idris Garba Tofawa, ya ce sun ɗauki lamarin a matsayin ƙaddarar Ubangiji, amma ya bukaci hukumomi da su ɗauki matakin gaggawa don hana maimaituwar irin wannan lamari.

Ya ce: “Muna roƙon a tabbatar da adalci, ba don ɗanmu kaɗai ba, har ma da lafiyar sauran dalibai gaba ɗaya.”

Yayin da ake ci gaba da bincike, Gwamnatin Kano ta sake jaddada kudirinta na kare lafiyar dalibai da kuma tabbatar da doka da oda a dukkan makarantun gwamnati.

Ana sa ran hukumomin tsaro za su ba da goyon baya wajen gudanar da binciken da kuma tabbatar da cewa an hukunta masu laifi.

 

Khadijah Aliyu

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara