Ilimi
Gwamnatin Jigawa Za Ta Katange Makarantun Sakandare Domin Samar Da Ingantaccen Yanayin Karatu
Gwamnatin Jihar Jigawa ta gudanar da bude tayin kwangila domin gina katanga, ƙofofi da gidajen masu gadi a wasu makarantun sakandare a fadin jihar.
A jawabinsa yayin gabatar da tayin, Shugaban Hukumar Manyan Makarantu na Jihar, Dakta Abubakar Sabo Yusha’u ya ce za a gina katanga da ƙofar shiga da gidan mai gadi a manyan makarantun sakandare ne domin kare makarantun daga mamayar filaye tare da samar da yanayin koyo da koyarwa mai kyau ga malamai da ɗalibai.
Dakta Abubakar Sabo Yushau ya bayyana cewa, ayyukan na daga cikin ajandar Gwamna Umar Namadi 12, wajen gyara sashen ilimi da inganta harkar koyo da koyarwa a makarantun jihar.

A cewarsa, manyan makarantun sakandare 15 ne za su ci gajiyar ayyukan, inda za a gina katanga, ƙofa da gidan mai gadi a kowace makaranta.
Ya kuma gode wa Gwamna Umar Namadi bisa jajircewarsa wajen inganta harkar ilimi a jihar.
Dakta Yushau ya bukaci waɗanda suka yi nasarar samun kwangilar da su ji tsoron Allah tare da tabbatar da ingantaccen aiki cikin wa’adin da aka kayyade.

A jawabansu, wakilan ƙungiyoyin kwararru na Due Process sun yi karin bayani kan ka’idoji da hanyoyin gudanar da tsarin kwangila, tare da kira ga ‘yan kwangila da su kiyaye dokokin tsarin kwangilar.
A jawabinsa na godiya a madadin hukumar, Daraktan Harkokin Gudanarwa da Kudi na, Malam Hussaini Ahmad Ubale ya gode wa hukumomi tare da yabawa kamfanonin da suka nuna sha’awa wajen shiga tsarin tayin kwangilar.
Usman Muhammad Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
