Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Jigawa Za Ta Katange Makarantun Sakandare Domin Samar Da Ingantaccen Yanayin Karatu

Published

on

Gwamnatin Jihar Jigawa ta gudanar da bude tayin kwangila domin gina katanga, ƙofofi da gidajen masu gadi a wasu makarantun sakandare a fadin jihar.

A jawabinsa yayin gabatar da tayin, Shugaban Hukumar Manyan Makarantu na Jihar, Dakta Abubakar Sabo Yusha’u ya ce za a gina katanga da ƙofar shiga da gidan mai gadi a manyan makarantun sakandare ne domin kare makarantun daga mamayar filaye tare da samar da yanayin koyo da koyarwa mai kyau  ga malamai da ɗalibai.

Dakta Abubakar Sabo Yushau ya bayyana cewa, ayyukan na daga cikin ajandar Gwamna Umar Namadi 12, wajen gyara sashen ilimi da inganta harkar koyo da koyarwa a makarantun jihar.

A cewarsa, manyan makarantun sakandare 15 ne za su ci gajiyar ayyukan, inda za a gina katanga, ƙofa da gidan mai gadi a kowace makaranta.

Ya kuma gode wa Gwamna Umar Namadi bisa jajircewarsa wajen inganta harkar ilimi a jihar.
Dakta Yushau ya bukaci waɗanda suka yi nasarar samun kwangilar da su ji tsoron Allah tare da tabbatar da ingantaccen aiki cikin wa’adin da aka kayyade.

A jawabansu, wakilan ƙungiyoyin kwararru na Due Process sun yi karin bayani kan ka’idoji da hanyoyin gudanar da tsarin kwangila, tare da kira ga ‘yan kwangila da su kiyaye dokokin tsarin kwangilar.

 

A jawabinsa na godiya a madadin hukumar, Daraktan Harkokin Gudanarwa da Kudi na, Malam Hussaini Ahmad Ubale ya gode wa hukumomi tare da yabawa kamfanonin da suka nuna sha’awa wajen shiga tsarin tayin kwangilar.

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai9 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara