Ilimi
Gwamnatin Jigawa ta Sami Gagarumin Cigaba a Bangaren Ilimi- Gwamna Namadi
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamnatin Jihar Jigawa ta ce jarin da take ci gaba da zubawa a bangaren ilimi ya fara haifar da sakamako mai kyau, musamman a matakin ilimin firamare a fadin jihar.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan yayin da ya jagoranci taron masu ruwa da tsaki a bangaren ilimin firamare, wanda aka shirya domin duba irin ci gaban da aka samu, kalubalen da ake fuskanta da kuma damar da ke akwai.
An gudanar da taron ne a Fadar Gwamnati da ke Dutse.
Gwamna Namadi ya nuna jin dadinsa da sakamakon taron, yana mai cewa bayanan da aka gabatar sun nuna tasirin jarin da gwamnati da abokan hulda ke zubawa a bangaren ilimi.

Ya ce gudummawar hukumomin bada tallafi da sauran abokan hulda, tare da kokarin gwamnati, na taimakawa matuka wajen inganta ilimi a fadin jihar.
Gwamnan ya yaba da jajircewar abokan hulda wajen inganta koyarwa da koyo. Haka kuma ya ba su tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da aiki tare da su, da kuma samar da yanayi mai kyau da zai ba su damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.
Ya kuma yi alkawarin cewa gwamnatin jihar za ta yi nazari kan dukkan shawarwari da gudummawar da aka bayar a taron, domin duba yiwuwar shigar da su cikin tsare-tsare da manufofin ilimi na jihar.
A nasa bangaren, Kwamishinan Ilimin Firamare, Dakta Lawal Yunusa Danzomo, ya bayyana cewa taron ya hada dukkan sassa da cibiyoyin da ke da alaka da tattara bayanan ilimi da kuma gudanar da ayyukan ilimi.
Ya jaddada cewa magance matsalolin bangaren ilimi na bukatar hadin kai daga dukkan masu ruwa da tsaki.

Danzomo ya kara da cewa manufar shirin ita ce tabbatar da cewa kowanne yaro a Jigawa ya shiga makaranta, tare da wucewa zuwa mataki na gaba ba tare da yankewa ba.
Ya ce binciken da aka yi a baya-bayan nan ya nuna an samu ci gaba wajen shigar yara makaranta, da ci gaban karatunsu zuwa mataki na gaba da kuma yawan wadanda ke kammala karatu. Haka kuma an samu ci gaba wajen daukar malamai aiki, turasu wuraren aiki, horas da su, halartar aiki, da kuma ingancin koyarwarsu.
Taron na daga cikin kokarin Gwamna Umar Namadi na farfado da bangaren ilimi da kuma mayar da shi ginshikin ci gaban al’umma a Jihar Jigawa.
Daga cikin kungiyoyi da abokan hulda da suka halarci taron akwai PLANE, AGILE, UNICEF, Bankin Raya Kasashen Musulmi (IDB), da Save the Children, da sauransu.
-
Labarai2 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
