Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Jigawa ta Sami Gagarumin Cigaba a Bangaren Ilimi- Gwamna Namadi

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin Jihar Jigawa ta ce jarin da take ci gaba da zubawa a bangaren ilimi ya fara haifar da sakamako mai kyau, musamman a matakin ilimin firamare a fadin jihar.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan  yayin da ya jagoranci taron masu ruwa da tsaki a bangaren ilimin firamare, wanda aka shirya domin duba irin ci gaban da aka samu, kalubalen da ake fuskanta da kuma damar da ke akwai.

 

An gudanar da taron ne a Fadar Gwamnati da ke Dutse.

Gwamna Namadi ya nuna jin dadinsa da sakamakon taron, yana mai cewa bayanan da aka gabatar sun nuna tasirin jarin da gwamnati da abokan hulda ke zubawa a bangaren ilimi.

Ya ce gudummawar hukumomin bada tallafi da sauran abokan hulda, tare da kokarin gwamnati, na taimakawa matuka wajen inganta ilimi a fadin jihar.

Gwamnan ya yaba da jajircewar abokan hulda wajen inganta koyarwa da koyo. Haka kuma ya ba su tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da aiki tare da su, da kuma samar da yanayi mai kyau da zai ba su damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Ya kuma yi alkawarin cewa gwamnatin jihar za ta yi nazari kan dukkan shawarwari da gudummawar da aka bayar a taron, domin duba yiwuwar shigar da su cikin tsare-tsare da manufofin ilimi na jihar.

A nasa bangaren, Kwamishinan Ilimin Firamare, Dakta Lawal Yunusa Danzomo, ya bayyana cewa taron ya hada dukkan sassa da cibiyoyin da ke da alaka da tattara bayanan ilimi da kuma gudanar da ayyukan ilimi.

Ya jaddada cewa magance matsalolin bangaren ilimi na bukatar hadin kai daga dukkan masu ruwa da tsaki.

Danzomo ya kara da cewa manufar shirin ita ce tabbatar da cewa kowanne yaro a Jigawa ya shiga makaranta, tare da wucewa  zuwa mataki na gaba ba tare da yankewa ba.

Ya ce binciken da aka yi a baya-bayan nan ya nuna an samu ci gaba wajen shigar yara makaranta, da ci gaban karatunsu zuwa  mataki na gaba da kuma yawan wadanda ke kammala karatu. Haka kuma an samu ci gaba wajen daukar malamai aiki, turasu wuraren aiki, horas da su, halartar aiki, da kuma ingancin koyarwarsu.

Taron na daga cikin kokarin Gwamna Umar Namadi na farfado da bangaren ilimi da kuma mayar da shi ginshikin ci gaban al’umma a Jihar Jigawa.

Daga cikin kungiyoyi da abokan hulda da suka halarci taron akwai PLANE, AGILE, UNICEF, Bankin Raya Kasashen Musulmi (IDB), da Save the Children, da sauransu.

 

 

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara