Connect with us

Ilimi

Gwamnatin Jigawa ta Sami Gagarumin Cigaba a Bangaren Ilimi- Gwamna Namadi

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnatin Jihar Jigawa ta ce jarin da take ci gaba da zubawa a bangaren ilimi ya fara haifar da sakamako mai kyau, musamman a matakin ilimin firamare a fadin jihar.

Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan  yayin da ya jagoranci taron masu ruwa da tsaki a bangaren ilimin firamare, wanda aka shirya domin duba irin ci gaban da aka samu, kalubalen da ake fuskanta da kuma damar da ke akwai.

 

An gudanar da taron ne a Fadar Gwamnati da ke Dutse.

Gwamna Namadi ya nuna jin dadinsa da sakamakon taron, yana mai cewa bayanan da aka gabatar sun nuna tasirin jarin da gwamnati da abokan hulda ke zubawa a bangaren ilimi.

Ya ce gudummawar hukumomin bada tallafi da sauran abokan hulda, tare da kokarin gwamnati, na taimakawa matuka wajen inganta ilimi a fadin jihar.

Gwamnan ya yaba da jajircewar abokan hulda wajen inganta koyarwa da koyo. Haka kuma ya ba su tabbacin cewa gwamnatin jihar za ta ci gaba da aiki tare da su, da kuma samar da yanayi mai kyau da zai ba su damar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.

Ya kuma yi alkawarin cewa gwamnatin jihar za ta yi nazari kan dukkan shawarwari da gudummawar da aka bayar a taron, domin duba yiwuwar shigar da su cikin tsare-tsare da manufofin ilimi na jihar.

A nasa bangaren, Kwamishinan Ilimin Firamare, Dakta Lawal Yunusa Danzomo, ya bayyana cewa taron ya hada dukkan sassa da cibiyoyin da ke da alaka da tattara bayanan ilimi da kuma gudanar da ayyukan ilimi.

Ya jaddada cewa magance matsalolin bangaren ilimi na bukatar hadin kai daga dukkan masu ruwa da tsaki.

Danzomo ya kara da cewa manufar shirin ita ce tabbatar da cewa kowanne yaro a Jigawa ya shiga makaranta, tare da wucewa  zuwa mataki na gaba ba tare da yankewa ba.

Ya ce binciken da aka yi a baya-bayan nan ya nuna an samu ci gaba wajen shigar yara makaranta, da ci gaban karatunsu zuwa  mataki na gaba da kuma yawan wadanda ke kammala karatu. Haka kuma an samu ci gaba wajen daukar malamai aiki, turasu wuraren aiki, horas da su, halartar aiki, da kuma ingancin koyarwarsu.

Taron na daga cikin kokarin Gwamna Umar Namadi na farfado da bangaren ilimi da kuma mayar da shi ginshikin ci gaban al’umma a Jihar Jigawa.

Daga cikin kungiyoyi da abokan hulda da suka halarci taron akwai PLANE, AGILE, UNICEF, Bankin Raya Kasashen Musulmi (IDB), da Save the Children, da sauransu.

 

 

Labarai

Ilimi15 hours ago

Dr. Builder Muhammad Uba Ya Jagoranci Rangadin Makarantu a Birnin Kudu

Daga Usman Muhammad Zaria Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu a Jihar Jigawa, Dakta Builder Muhammad Uba ya bayyana ilimi a...

Labarai2 days ago

Masarautar Saminaka ta Bukaci Hadin Kai Don Dorewar Zaman Lafiya a Yankin

Daga Yusuf Zubairu Majalisar Masarautar Saminaka da ke Jihar Kaduna ta yi kira ga al’ummomin da ke Karamar Hukumar Lere...

Labarai2 days ago

Hukumar Alhazai ta Jihar Jigawa ta Kammala Shirin Rigakafi ga Maniyyatan Bana

Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta kammala tanadin katin shaidar rigakafin cututtuka ga dukkan maniyyatan aikin Hajjin shekarar...

Labarai2 days ago

NEMA ta Karbi ‘Yan Najeriya 522 da Aka Dawo da su Daga Jamhuriyar Nijar

Daga Khadijah Aliyu Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta karɓi wani rukuni na ’yan Najeriya 522 da...

Labarai2 days ago

Za mu kai hari kan gidajen jami’an Amurka da Isra’ila – Iran

Hedikwatar Khatam al-Anbiya, wacce ita ce babbar cibiyar da ke kula da daidaita ayyukan rundunonin sojin Iran, ta yi barazanar...

Labarai2 days ago

Radio Nigeria @75: Tsohon Dan Jarida Ya Yi Waiwaye Kan Tarihi Radio Nijeriya

An bayyana cikar shekaru 75 da kafuwar Radio Nigeria a matsayin wani babban mataki wajen gina ci gaban zamantakewa, tattalin...

Labarai2 days ago

Ɗaya Daga Cikin Jariran nan Biyar Ya Rasu, Huɗu Na Ci Gaba Da Jinya a Asibitin Kano

Hukumar Kula da Asibitocin Jihar Kano ta tabbatar da rasuwar ɗaya daga cikin jarirai biyar da aka haifa a Asibitin...

Labarai2 days ago

Shugaba Tinubu Ya Sadaukar Da Albashinsa Domin Sabon Asusun Tallafi Ga Sojoji

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da kafa wani asusun tallafi na musamman domin taimaka wa jami’an rundunar sojin...

Labarai2 days ago

FMC Gusau ta karɓi tallafin littattafan lafiya daga gidauniyar Sir Emeka Offor

Asibitin Kula da Lafiya na Tarayya da ke Gusau, ya karɓi tarin littattafan kiwon lafiya da mujallu daga Sir Emeka...

Labarai2 days ago

NIPHID ta gudanar da gangamin wayar da kai kan tarin fuka a Zaria, Kaduna

Cibiyar kula da lafiya dake Saye Zaria, ta gudanar da gangamin wayar da kai kan cutar tarin fuka (TB) a...

Mafi Shahara