Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jigawa Ta Kaddamar Da Harsashin Ginin Dindindin Na Kwalejin Jinya Ta Hadejia

Published

on

Gwamna Umar Namadi na jihar Jigawa ya kaddamar da bikin aza harsashin gina rukunin dindindin na kwalejin  jinya da ungozoma da ke Hadejia na naira biliyan biyar da rabi domin samar da isassun ma’aikata da kwararru a fannin lafiya.

Gwamnan ya bayyana cewa ingantaccen tsarin kiwon lafiya wani muhimmin alkawari ne da aka yi gabanin zabe wanda aka sanya shi cikin tsare-tsare guda 12 don ci gaban jihar Jigawa baki daya.

Ya ce aikin wanda ya kasu kashi biyu, ana sa ran kammala shi a cikin watanni 18 inda za a kashe naira biliyan 3 da kuma Naira biliyan 2 da rabi bi da bi.

Mallam Umar Namadi ya ci gaba da cewa, gwamnatin sa ta kuma yi niyyar samar da babban asibiti  a kowace mazabar majalisar jiha 30 da kuma cibiyar kula da lafiya a matakin farko a kowace gunduma.

Ya ce, wannan kari ne ga asibitocin kwararru da aka kafa a  shiyyoyi  t3 na jihar.

Namadi ya kuma ce, domin tabbatar da isassun ma’aikatan lafiya, gwamnati ta tura sama da dalibai 109 zuwa kasar Cyprus don yin karatun likitanci, tare da karin karatu a cikin gida.

Ya yi nuni da cewa, akwai kwalejojin aikin jinya da ungozoma guda uku a Birninkudu, Babura, da Hadejia, Gwamnan ya ce yana da kwarin guiwar samun ma’aikatan lafiya kwararru.

 

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai10 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara