Labarai
Gwamnatin Jigawa Ta Haramta Noma A Dukkan Dazukan Gwamnati
Gwamnatin Jihar Jigawa tace ta kwace dazukan gwamnati a hannun jama’a, za kuma a bada aron su ga jama’a domin yin noma.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan a lokacin hawan bariki da mai martaba sarkin Dutse ya kai masa a gidan Gwamnati.

Malam Umar Namadi, yace Gwamnatin jihar ta kwace duk wani daji da makiyayu da burtalai da aka bayar ba bisa ka’ida ba, tare da haramta yin noma a cikin su.
Yana mai cewa an kafa kwamiti domin duba wannan lamari kuma tuni kwamitin ya bada rahotan wucin gadi.

Ya ce shugabannin kananan hukumomi da Hakimai da Dagatai da masu unguwanni su ne babbar matsalar dake tattare da matsalar dazuka a jihar Jigawa.
A don haka, Namadi ya yi gargadin cewa duk shugaban karamar hukuma ko Hakimi ko Dagaci ko mai unguwa da aka samu ya bada daji ba bisa ka’ida ba zai fuskanci fushin hukuma.

Yayi nuni da cewar gwamnati zata kai doka majalissar dokokin jihar domin hana sarar itatuwa a fadin jihar jigawa.

Da ya waiwayi batun takin zamani kuwa, Gwamnan ya ce Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bada takin zamani tirela 80 domin rabawa al’ummar jihar Jigawa kyauta.
Kazalika, ya ce itama gwamnatin jihar ta siyo takin domin sayarwa manoma a farashi mai sauki.

Gwamna Namadi ya ce an kafa kwamiti domin sa ido wajen rabon takin zamanin na shugaban kasa da kuma wanda gwamnatinsa za ta sayarwa manoma.
Usman Mohammed Zaria
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
