Ilimi
Gwamnatin Jigawa Ta Bada Kwangilar Hanyar Kiyawa Zuwa Birnin Kudu
Gwamnatin jihar Jigawa ta ce za ta bayar da kwangilar aikin sake gina titin Kiyawa zuwa Birnin kudu.
Gwamna Umar Namadi ya bayyana hakan a lokacin da ya kai ziyarar duba hanyar.
Gwamnan ya nuna rashin jin dadinsa da jinkirin da ake yi na gyaran hanyar da kuma sake gina magudanan ruwa a hanyar da aka bayar a bara.
Don haka Mallam Umar Namadi ya yi kira ga dan kwangilar da ke gudanar da aikin da ya gaggauta daukar mataki tare da kammala aikin kamar yadda aka tsara.
Gidan Rediyon Najeriya na Kaduna ya ruwaito cewa, Gwamnan ya kuma kai ziyarar gani da ido kan aikin titin Shuwarin, Wurma, Abaya da kuma Chamo zuwa Isari da ake yi.
Ya kuma ziyarci makarantar firamare ta Shuwarin Yamma da cibiyar kula da lafiya a matakin farko inda ya tattauna da malamai da ma’aikatan lafiya kan yadda za a tabbatar da ingancin aikin.
KARSHE/USMAN MZ/Wababe
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
