Connect with us

Labarai

Gwamnan Zamfara Na Nan Daram A PDP – Dantawasa

Published

on

Gwamnatin jihar Zamfara ta musanta ikirarin da ke yawo a wasu bangarori na cewa, Gwamna Dauda Lawal na shirin sauya sheka zuwa jam’iyyar APC, yana mai bayyana jita-jitan a matsayin maras tushe, balle makama, kuma aikin ‘yan adawa ne.

 

A wata sanarwa da kwamishinan yada labarai da al’adu na jihar, Mahmud Muhammad Dantawasa ya fitar, ya ce wasu mutane ne da ke neman a ci gaba da damawa da s uke yawo da wannan zancen bayan da jama’a sun ki amincewa da wannan labarin.

 

Sanarwar ta bayyana wannan jita-jita a matsayin karya, abin dariya, da kuma matsanancin yunƙuri na ƴan adawa da ke hasken s uke dushewa.

 

Ta ce yadda Gwamna Lawal ya samu sauyi da jajircewarsa na sake gina Zamfara ya sa ya samu karbuwa sosai, har ma da abokan hamayyar siyasa.

 

“Ba abin mamaki ba ne cewa ‘yan jam’iyyar APC, musamman wadanda suka haddasa rugujewar shekara da shekaru a Zamfara, suna zawarcin Gwamna Lawal.

 

“Amma a fayyace cewa shi dan jam’iyyar PDP ne, mutum ne mai kishin kasa wanda ba zai yi watsi da jam’iyyar da ta ba shi ikon ceto jihar ba, ko da kuwa wace irin jarabawar ce ake fuskanta.”

 

Sanarwar ta kuma bayyana cewa, Gwamna Lawal na kan hanyarsa ta zuwa Abuja ne domin halartar taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar PDP na kasa (NEC), inda ya jaddada kudirinsa na tabbatar da kimar jam’iyyar da manufofinta.

 

 

REL/AMINU DALHATU.

Labarai

Labarai6 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara