Labarai
Gwamnan Kano Ya Yi Rangwamen Kashi 50 Bisa 100 Na Takin Zamani
Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya raba tireloli uku uku na taki ga Kananan Hukumomin jihar 44, tare da yin rangwamen kashi hamsin bisa dari na kudaden takin ga manoma.
Kowacce tirela tana ɗauke da buhuna 600 na taki, wanda ya kai jimillar buhuna 79,200.
An kaddamar da bikin rabon takin ne a harabar kamfanin Al Yuma Fertilizer da ke karamar hukumar Madobi.
Gwamna Yusuf ya jaddada muhimmancin noma wajen ci gaban jihar, inda ya ce: “Mun taru a nan ba kawai don raba buhunan taki ba, sai don tabbatar da kara inganta dogaro da kai, da habbaka tattalin arzikin.”
Gwamnan ya bayyana wasu daga cikin nasarorin da gwamnati ta samu a fannin bunkasa noma, wadanda suka haɗa da faɗaɗa damar samar da filayen noma, da habbaka noman rani , da kuma bayar da sabbin ayyuka a kananan hukumomi 11.
Haka kuma, ya ambaci gina dam a Dansoshiya da ke karamar hukumar Kiru, domin tallafa wa aikin noma.
Ana sa ran yin rangwamen kashi hamsin bisa dari a kan takin zai ƙara samar da abinci, habaka tattalin arziki, da wadatar abincin a jihar.
Gwamna Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa rabon taki a farkon damina ya zo a kan lokaci, wanda tabbas zai amfani manoma.
Abdullahi Jalaluddeen
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai5 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai7 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai1 day agoGwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu
-
Labarai4 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
