Ilimi
Gwamnan Kano Ya Bada Umarnin Bincika Zargin Zaftare Albashin Ma’aikatan Gwamnati.
Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano ya yi wani kakkausan gargadi game da rahotannin rashin biyan albashi da rashin biyan ma’aikatan jihar, inda ya bayyana hakan a matsayin tauye hakkin ma’aikata da kuma cin amanar jama’a.
Gwamnan ya bayyana haka ne a lokacin da yake kaddamar da kwamitin bincike mai mutane bakwai, karkashin jagorancin Hon. Abdulkadir Abdussalam, domin gano musabbabin sabanin.
Sakataren gwamnatin jiha Alhaji Umar Faruk ya wakilta, ya ce kwamitin ya hada da manyan jami’an gwamnati da masana harkokin kudi da wadanda suka kware a tsarin biyan albashi.
Yace Membobin Kwamitin sune Abdulkadir Abdussalam_ – Shugaban, Kwamishinan Karkara da Ci gaban Al’umma Dr. Bashir Abdu Muzakkari – memba, mai ba da shawara na musamman kan tattalin arzikin dijital, Dr. Aliyu Isa Aliyu – Memba, Darakta-Janar na Ofishin Kididdiga na Jihar Kano.
Dokta Hamisu Sadi Ali, Memba, Babban Darakta Janar na Ofishin Kula da Bashi na Jihar Kano, Hajiya Zainab Abdulkadir – Mamba, Darakta, Cibiyar Kwamfuta ta Jihar Kano, Aliyu Muhammad Sani – Sakatare, Darakta, Bincike da Aiki na Hukumar REPA, Ofishin SSG.
Ummulkulthum Ladan Kailani – zata kasance mataiamakiyar sakataren kwamitin.
Ya ce an baiwa kwamitin kwanaki bakwai don gabatar da cikakken rahoto.
Gwamnan ya kuma tabbatar wa da ma’aikatan gwamnati cewa gwamnatinsa ta himmatu wajen tabbatar da adalci, gaskiya da kuma biyan albashi cikin gaggawa, yana mai gargadin cewa duk wanda aka samu da laifin cin zarafin ma’aikata zai fuskanci mummunan sakamako.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
