Labarai
Gwamna Namadi Ya Rattaba Hannu Kan Kasafin Shekarar 2026
Daga Usman Muhammad Zaria
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya rattaba hannu kan kasafin kuɗin shekarar 2026 na Naira biliyan 901 da miliyan 804, domin inganta ci gaban jihar tare da biyan buƙatun al’ummar Jigawa.
Da yake jawabi bayan sanya hannu kan kasafin, Gwamna Namadi ya bayyana cewa duk da kasafin jihar ya kai sama da Naira Biliyan, kasafin kuɗin haɗin gwiwa na ƙananan hukumomi 27 ya kai Naira Biliyan 288 da Miliyan 805.
“Wannan kasafi sakamakon shirin tattaunawa da al’umma ne da muka gudanar, kuma yana nuna ainihin muradu da burin mutanen Jihar Jigawa.

“Saboda haka, kasafin al’umma ne, daidai yadda jama’a suka buƙata, kuma daidai abin da ke ƙunshe a cikin wannan kasafi,” in ji gwamnan.
Gwamnan ya kuma yabawa mambobin Majalisar Dokokin Jihar Jigawa bisa jajircewa da sadaukarwar da suka nuna a duk tsawon aikin kasafin kuɗin.

“Goyon bayansu a yayin tarukan tattaunawa da al’umma, ganawar bangarori biyu, tattaunawa ta manyan shugabanni, da kuma matakan kwamitoci, ya taka muhimmiyar rawa wajen amincewa da wannan kasafi cikin nasara,” in ji shi.
Gwamnan ya kuma yabawa mambobin Majalisar Zartarwa ta Jihar bisa amincewa da kuma shiga shirin tattaunawa da al’umma, tare tattara ra’ayoyin jama’a, inda da dama daga cikinsu ke aiki har cikin dare.

Haka nan, Namadi ya yaba wa al’ummar jihar bisa goyon baya da kuma halartar su a tsarin kasafin kuɗin, inda ya yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta yi iya ƙoƙarinta wajen inganta rayuwar al’ummar Jigawa.
-
Labarai3 days agoIran ta Tabbatar da Kisan Ayatollah Khamenei a Hare-haren Amurka da Isra’ila
-
Labarai4 days agoMajalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince da Kasafin Kudin Kananan Hukumomin Jihar na 2026
-
Labarai4 days agoAzumin Ramadan: Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu Ya Bada Tallafin Kudi ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoUwargidan Gwamnan Zamfara Ta Kaddamar da Rabon Tallafin Ramadan ga Marasa Galihu
-
Labarai6 days agoWani Bam Kirar Hannu Ya Fashe a Kan Hanyar Gusau Zuwa Funtua
-
Labarai3 days agoBankin Raya Kasashen Afirka Zai Samar da Shirin Bunƙasa Aikin Noma a Jigawa
-
Labarai3 days agoGwamnatin Jigawa ta Gargadi ‘Yan Kwangila Kan Ingancin Abincin Ramadan
-
Labarai3 days agoMasarautar Hadejia ta Raba Zakkar Kayan Amfanin Gona da Dabbobi a Garin Unik
