Connect with us

Labarai

Gwamna Namadi Ya Rattaba Hannu Kan Kasafin Shekarar 2026

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya rattaba hannu kan kasafin kuɗin shekarar 2026 na Naira biliyan 901 da miliyan 804, domin inganta ci gaban jihar tare da biyan buƙatun al’ummar Jigawa.

Da yake jawabi bayan sanya hannu kan kasafin, Gwamna Namadi ya bayyana cewa duk da kasafin jihar ya kai sama da Naira Biliyan, kasafin kuɗin haɗin gwiwa na ƙananan hukumomi 27 ya kai Naira Biliyan 288 da Miliyan 805.

Wannan kasafi sakamakon shirin tattaunawa da al’umma ne da muka gudanar, kuma yana nuna ainihin muradu da burin mutanen Jihar Jigawa.

Saboda haka, kasafin al’umma ne, daidai yadda jama’a suka buƙata, kuma daidai abin da ke ƙunshe a cikin wannan kasafi,” in ji gwamnan.

Gwamnan ya kuma yabawa mambobin Majalisar Dokokin Jihar Jigawa bisa jajircewa da sadaukarwar da suka nuna a duk tsawon aikin kasafin kuɗin.

Goyon bayansu a yayin tarukan tattaunawa da al’umma, ganawar bangarori biyu, tattaunawa ta manyan shugabanni, da kuma matakan kwamitoci, ya taka muhimmiyar rawa wajen amincewa da wannan kasafi cikin nasara,” in ji shi.

Gwamnan ya kuma yabawa mambobin Majalisar Zartarwa ta Jihar bisa amincewa da kuma shiga  shirin tattaunawa da al’umma, tare tattara ra’ayoyin jama’a, inda da dama daga cikinsu ke aiki har cikin dare.

Haka nan, Namadi ya yaba wa al’ummar jihar bisa goyon baya da kuma halartar su a tsarin kasafin kuɗin, inda ya yi alkawarin cewa gwamnatinsa za ta yi iya ƙoƙarinta wajen inganta rayuwar al’ummar Jigawa.

 

Labarai

Labarai8 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai2 days ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai2 days ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai2 days ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara