Connect with us

Kasuwanci

Gwamna Namadi Ya Kaddamar da Tallafin Miliyoyin Naira Ga Ƴan NURTW da Mahauta a Jigawa

Published

on

Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da shirin tallafi guda biyu da suka kai fiye da naira miliyan 392, ga membobin kungiyar direbobi ta NURTW da kuma ƴan kungiyar mahauta a jihar Jigawa.

Wannan tallafi wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta rayuwar masu sana’o’in  da ke taka muhimmiyar rawa a rayuwar yau da kullum.

A wajen kaddamar da shirin a filin wasa na Dutse, Gwamna Namadi ya bayyana cewa shirin yana da manufa ta musamman domin tallafa wa jama’a kai tsaye. Ya ce ƙungiyoyin NURTW da mahauta suna da matuƙar tasiri, ba kawai ga membobinsu ba, har ma da al’umma gaba ɗaya, shi ya sa gwamnatinsa ta ga dacewar tallafa musu.

Gwamnan ya kara da cewa taimakon da aka bai wa waɗannan ƙungiyoyi zai kara habaka tattalin arzikin al’ummar jihar. Ya yabawa ƙungiyoyin bisa yadda suka tsaya tsayin daka wajen kare muradun membobinsu.

Ya bukaci shugabannin ƙungiyar da su tabbatar da sa ido sosai da kuma ganin cewa an bi dukkan sharuddan shirin. “Hakan zai tabbatar da cewa motocin sun yi aiki daidai da manufa, tare da bai wa shirin damar dorewa da kuma faɗaɗawa don amfanar da wasu a nan gaba’. In ji shi. 

Gwamnan ya yaba da rawar da NURTW ke takawa a tattalin arzikin jihar, yana mai bayyana su a matsayin muhimmin ɓangare na samar da kayayyaki, ko a fannin noma, masana’antu ko kasuwanci. Ya ce babu wata harkar rarraba kaya da za ta yi tasiri ba tare da haɗin guiwar NURTW ba.

A cewarsa, gwamnatinsa na saka jari mai yawa a fannin gina hanyoyin mota, inda aka kammala ayyukan hanya guda 26 da aka gada, da kudin da ya kai sama da naira biliyan 100. Haka kuma, an ƙara bayar da kwangiloli don gina tituna 50 masu tsawon fiye da kilomita 850, da kudinsu ya haura naira biliyan 300.

Gwamnan ya bayyana cewa an fara amfani da hanyoyin makamashi masu tsafta, inda aka kusa kammala cibiyar sauya motoci zuwa CNG a jihar. Ya ce wannan cibiya za ta taimaka matuƙa wajen rage farashi da kuma tsaftace muhalli, tare da fa’ida kai tsaye ga ƴan NURTW.

A wani ɓangare na shirin, Gwamna Namadi ya kaddamar da tsarin lamuni na naira miliyan 113 ga ƴan kungiyar mahauta. Shirin zai taimaka wa mutane 53, inda manyan ‘yan kasuwar dabbobi 15 za su samu naira miliyan 5 kowanne, sai sauran 38 da za su samu miliyan 1 kowanne.

Ya ce ana sa ran wannan tallafi zai taimaka wajen bunkasa harkar kiwon dabbobi da samar da nama a jihar, har da kasuwannin nama gaba ɗaya.

Don tabbatar da dorewar wannan ci gaba, gwamnan ya bayyana shirin kafa sabuwar ma’aikatar ci gaban kiwo a jihar.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa a matakin farko na shirin, an raba motoci 36 na kasuwanci da darajarsu ta kai naira miliyan 279.3, tare da inshora, ga membobin NURTW karkashin tsarin lamuni na juyi da hukumar Youth Economic Empowerment da Employment ta jihar ke jagoranta.

 

Usman Muhammad Zaria

Labarai

Labarai4 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai1 day ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara