Connect with us

Labarai

Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Aikin Gina Hanyoyi Ba Naira Biliyan 81 A Malam Madori

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya jaddada kudirin gwamnatin sa na ci gaba da bunkasa hanyoyin sufuri a fadin jihar.

Gwamnan ya bayyana hakan ne yayin da ya kaddamar da wani muhimmin aikin gina hanyoyi a karamar hukumar Mallam Madori.

Yayin taron kaddamarwar, Gwamna Namadi ya bayyana cewa aikin yana cikin shirin “Gwamnati da Jama’a” wanda ke karfafa al’umma, rage matsalolin sufuri da kuma karfafa harkokin kasuwanci.

Ya ce shirin ya kunshi gina manyan hanyoyi guda shida a sassan jihar, masu tsawon kilomita 179 gaba daya, a kan kudin da ya haura Naira Biliyan 81.

Hanyoyin sun hada da Mallam Madori zuwa Gari Uku zuwa Kanya Babba zuwa Malorin Kasim, ta ratsa ta Abori Sumburtu, har zuwa Diginsa, mai tsawon kilomita talatin da hudu da rabi.

Sai kuma hanyar Arbus zuwa Girbobo zuwa Garin Bukar mai nisan kilomita talatin da uku da rabi.

Kazalika akwai hanyar Dundubus zuwa Yanjaji zuwa Wangara mai tsawon kimanin kilomita goma sha bakwai.

Akwai kuma hanyar Jahun zuwa Takalafiya zuwa Zareku zuwa Kafin Hausa da reshe daga Takalafiya zuwa Dangyatum mai kilomita talatin da takwas.

Da hanyar Kukayasku zuwa Malamaba zuwa Katuka zuwa Garin Kwalandi mai nisan kilomita talatin da hudu da rabi.

Sai cikon ta shidda wacce ta tashi daga Farun Daba zuwa Maitsani zuwa Baauzini zuwa Kafin Chiroma zuwa Gallu Babba zuwa Gallu Karama ta kai ga Karkarna Bypass mai nisan kilomita goma sha uku.

Gwamnan ya bayyana cewa tuni an yi kashi 35 cikin 100 aikin,  yana mai fatan cewa za a gama shi cikin shekara guda, kafin wa’adin watanni 18.

Ya tabbatar da cewa gwamnatin sa za ta ci gaba da baiwa ababen more rayuwa, ilimi, kiwon lafiya, noma da samar da ayyukan yi muhimmanci a karkashin Manufofi 12 na Gwamnati don Cigaban Jigawa.

Ya kuma gode wa Gwamnatin Tarayya a karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu bisa tallafi da daidaiton manufofi.

A yayin ziyarar, Gwamna Namadi ya kuma kaddamar da sabon masallaci da aka gina a Garin Gabas, wanda shugaban karamar hukuma ya tallafa wajen ginawa.

Shugabannin al’umma sun mika wa Gwamnan kundin bukatun jama’a a matsayin wani bangare na tsarin mulkin jin ra’ayin al’umma.

Labarai

Labarai2 hours ago

Hukumar Kula da Kogin Benuwe ta Dauki Matakin Yashe Laka da Yashi da ke Barazana ga Noman Rani

Ayyukan ban ruwa a yankin Kogin Benuwe na fuskantar barazana sakamakon taruwar Laka da Yashi a kogin, lamarin da ke...

Labarai22 hours ago

Gwamna Namadi Ya Raba Tallafin Ramadan ga Ma’aikata da Marasa Galihu

Daga Usman Muhammad Zaria Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya raba tallafin kayan abinci na watan Ramadan tare da...

Labarai1 day ago

Sojoji Sun Yi Nasarar Kwato Dabbobi 257 da Aka Sace a Karamar Hukumar Gwarzo

Daga Abdullahi Jalaluddeen Sojojin Najeriya sun sami nasarar dawo da Shanu da Awaki  257 da aka sata a  wani aikin...

Labarai1 day ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara ta Yaba da Yadda Aka yi Rabon Tallafin Ramadan

Daga Aminu Dalhatu  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa dukkan masu ruwa da tsaki bisa...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kebbi Za ta Raba Hatsi da Kayayyakin Aikin Gona ga Marasa Galihu

Daga Sani Dutsinma Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen raba kayayyakin aikin noma da nau’o’in hatsi daban-daban ga mutane miliyan...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Kwara Ta Jaddada Kudurinta Na Kula Da Jin Daɗin Masu Harkar Sufuri

Gwamnatin Jihar Kwara ta bai wa masu harkar sufuri a jihar tabbacin ci gaba da kare muradunsu da jin daɗinsu....

Labarai1 day ago

Gwamnan Zamfara Ya Haramta Karbar Kudin Haraji A Hannu

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayar da umarnin dakatar da duk wani tsarin karbar kuɗaɗen shiga ta tsabar kuɗi...

Labarai1 day ago

Gwamnatin Tarayya Ta Faɗaɗa Rijistar Tallafin Jama’a Domin Tantance Masu Buƙata

Gwamnatin Tarayya na faɗaɗa tare da ƙarfafa Rijistar Tallafin Jama’a ta Ƙasa National Social Register domin tabbatar da cewa an...

Labarai1 day ago

Gwamna Idris Ya Ba da Umarnin Binciken Gobarar da Ta Tashi a Makarantar Nurul Haqq da ke Birnin Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya bayar da umarnin gaggauta kafa wani kwamitin bincike mai ƙarfi domin gano musabbabin gobarar...

Labarai1 day ago

Taraba Ta Kaddamar da Rarraba Kayan Aikin A Kananan Hukumomi 16

Hukumar Kula da Ci gaban Kiwon Lafiyar Matakin Farko ta Jihar Taraba ƙarƙashin Shirin IMPACT, ta ƙaddamar da rarraba kayan...

Mafi Shahara