Connect with us

Labarai

APC Ta Yi Gangamin Karfafa Hadin Kan Mambobinta Bayan Kaddamar Da Aikin Titin Malam Madori

Published

on

Daga Usman Muhammad Zaria 

Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya kaddamar da aikin gina hanya da kudinta ya kai Naira Biliyan 14 a Karamar Hukumar Malam Madori, wanda ke nuna jajircewar gwamnatinsa wajen bunkasa ababen more rayuwa1 karkashin shirin sabunta kudurori na gwamnatin tarayya wato “Renewed Hope Agenda.”

A yayin taron kaddamarwar, an kuma gabatar da sabbin motoci ga shugabannin jam’iyyar APC guda takwas da masu tallata jam’iyyar a mazabar Arewa maso gabashin jihar, wanda Sanata Ahmed Abdulhamid Malam Madori ya dauki nauyi.

Wannan mataki na da nufin karfafa hadin kai a jam’iyyar da kuma tallata hangen nesa na Shugaba Bola Ahmed Tinubu a fadin jihar.

A jawabinsa, Gwamna Namadi ya yaba da jajircewar Sanata Ahmed Malam Madori na nuna biyayya, karamci, da sadaukarwa wajen ci gaban jam’iyyar APC. “Wannan babbar shaida ce ta jajircewar Sanata Malam Madori ga jam’iyyarmu”.

 

Haka kuma Gwamnan ya karfafa gwiwar sauran mambobi da su tallafa wa shirin ci gaba na Shugaba Tinubu karkashin ‘Renewed Hope Agenda.”

Sanata Ahmed Abdulhamid Malam Madori ya bayyana cewa tallafin motocin na nufin bai wa mambobin jam’iyya damar yin ingantaccen aiki wajen tallata shirin ci gaba na Shugaban kasa da kuma Shirin Ci Gaba na Gwamna Namadi.

Shugaba Tinubu da Gwamna Namadi sun kawo gagarumin ci gaba ga al’umma da ababen more rayuwa a Jigawa. An amince da kafa muhimman hukumomin tarayya, ciki har da Cibiyar Horar da ‘Yan Sanda a Kafin Hausa, Kwalejin Ilimi ta Tarayya a Malam Madori, da Kwalejin Noma ta Tarayya a Kirikasamma,” in ji shi.

Ya jaddada ayyukan Gwamna Namadi na baya-bayan nan, ciki har da aikin hanyar kilomita 47 da ke hada Hadejia–Garun Gabas, inganta asibitoci, da farfado da cibiyoyin lafiya na farko.

Sanata Malam Madori ya kara da jaddada hadin kan masu ruwa da tsaki na APC a mazabar Arewa maso gabashin Jigawa, wanda ya hada da ‘yan majalisar wakilai guda uku, ‘yan majalisar jihar guda tara, shugabannin kananan hukumomi takwas, da ‘yan majalisar kananan hukumomi 85

Labarai

Ilimi1 day ago

SUBEB da UNICEF Sun Horas da Malaman Firamare a Jigawa

Hukumar Ilimin Bai Daya ta Jihar Jigawa (SUBEB), tare da haɗin gwiwar Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin...

Ilimi2 days ago

Majalisar Matan Shugabannin Afirka Ta Karrama Oluremi Tinubu Kan Ayyukan Tallafa wa Mata da Yara

Daga Bello Wakili  Majalisar Matan Shugabannin Kasashen Afirka OAFLAD ta karrama  Uwargidan Shugaban Ƙasar Nijeriya, Oluremi Tinubu  sakamakon gudunmawar da...

Labarai2 days ago

CAN A Jihar Niger Ta Yi Watsi Da Dokar Hisbah

Ƙungiyar Kiristoci ta Nijeriya reshen Jihar Niger State ta yi watsi da dokar Hisbah da Majalisar Dokokin Jihar Niger ta...

Labarai2 days ago

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Aikin Sake Gina Gadar Namnai A Taraba

Gwamnatin Tarayya, ta hannun Hukumar Raya Yankin Arewa maso ta fara aikin sake gina gadar Namnai da ta rushe a...

Labarai2 days ago

Netanyahu Ya Buƙaci A Kwashe Dukkan Uranium Din Iran Kafin Yarjejeniyar Nukiliya

Firaiministan Isra’ila ya buƙaci cire dukkan sinadarin uranium da aka samar daga Iran a matsayin wani ɓangare na yarjejeniyar Nukiliya...

Kasuwanci2 days ago

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya Ta Yi Alhini Ga Waɗanda Suka Rasu A Hare-Haren Ta’addanci

Kungiyar Gwamnonin Nijeriya ta bayyana damuwarta kan harin ta’addanci da aka kai daren Asabar a wasu al’umma uku na Tunga-Makeri,...

Labarai2 days ago

Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano Ja Jajanta Wa Waɗanda Gobarar Kasuwar Singa Ta Shafa

 Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kano, Jibril Ismail Falgore, ya miƙa ta’aziyyarsa ga Gwamnatin Jihar Kano, ’yan kasuwa da mazauna birnin...

Labarai2 days ago

Kungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah Ta Soki Matakin Majalisar Dokokin Amurka

Ƙungiyar Makiyaya ta Miyetti Allah ta Nijeriya (MACBAN) ta soki matakin da Majalisar Dokokin Amurka ta ɗauka na shirin ayyana...

Labarai2 days ago

Uwargidan Gwamnan Zamfara Ta Yabawa Tallafin jin-ƙai ga iyalai masu rauni gabanin Ramadan

  Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara State, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, ta yaba wa Hajiya Binta Lawal Barau Bungudu, matar Kwamishinan...

Labarai2 days ago

BUK Ta Musanta Zarge-Zargen Cin Hanci Kan Tsohon Shugaban Sashen Kula Da Ɗalibai

Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ta musanta zarge-zargen cin hanci da aka yi wa tsohon Shugaban Sashen kula da...

Mafi Shahara